Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran ya jaddada cewa: Iran ba za ta daina sarrafa sinadarin Uranium a kowane hali ba

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran Isma’il Baqa’i ya tabbatar a wata hira da tashar CNN ta Amurka cewa: Iran ba za ta taba yin watsi da hakkinta na tace sinadarin Uranium a kowane hali ba.

A yayin da yake mayar da martani game da kyakkyawan fata na shugaban Amurka Donald Trump game da shawarwarin nukiliyar da aka yi tsakanin gwamnatinsa da Iran da kuma yadda yake kallon ci gaban da aka cimma, Baqa’i ya ce: Idan manufar Amurka ita ce tabbatar da cewa shirin makamashin nukiliyar Iran ba zata yi amfani da shi wajen karfin soji ba, to yana ganin za a iya cimma hakan cikin sauki. To amma idan har Amurka tana son tauye wa Iraniyawa ‘yancinsu na samun cikakken fasahar makamashin nukiliya na zaman lafiya da lumana ne, to yana ganin hakan zai zama babbar matsala, ta yadda Iran za ta kalubalanci dukkan tsarin.

A lokacin da wakilin tashar CNN ya tambaye shi: Shin ko suna tsammanin gwamnatin Trump da mai shiga tsakaninta, Witkoff, sun gane kuma sun fahimci hakan? Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran ya mayar da martani da cewa: Kasancewar Iran tana ci gaba da tattaunawa ya zuwa yanzu tana nufin cewa ta san akwai wani matakin fahimtar da Iran ba za ta iya ba a kowane irin yanayi ta yi watsi da haƙƙinta na mallakar fasahar makamashin nukiliya na zaman lafiya da lumana da suka haɗa da inganta sinadarin Uranium.

Amurka

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaban Jam’iyyar Adawa A Burtaniya Ya Ce HKI Tana Yaki A Gaza Ne A Madadin Gwamnatin Kasar

Shugaban wata jam’iyyar adawa a kasar Burtaniya ya bayyana cewa HKI tana yakar Falasdinawa a Gaza ne a madadin gwamnatin kasar tunda har yanzun gwamnatin kasar Burtaniya tana ganin gwamnatin HKI tana kare kanta daga mayakan Hamas, kuma bata daukar abinda HKI take yi a Gaza, kissan kiyashi ne.

Badenoch shugaban jam’iyyar ‘ Conservative’ ya bayyana haka ne a lokacinda yake hira da tashar talabijin ta Sky News dake birnin London a jiya Lahadi.

A lokacinda aka tambaye shi idan ya yarda da maganar Banyamin natanyaho kan cewa hamas yan ta’adda ce, kuma yana kokarin kwace gaza da shafi yan ta’adda ne, sai shugaban Conservative ya ce banzo nan don binciken kalmomin Natanyahu ba. Abinda nake son bada sanarwansa shi ne HKI tana yaki ne a madadin gwamnatin kasar Burtaniya, kamar yadda kasar Ukraine take yakar kasar Rasha a madadin kasashen turai.

Banda haka gwamnatin ta ki ta aibata HKI sannan bata yarda cewa cewa tana aikata kissan kiyashe ne a gaza ba.

Shugaban conservative yana fadar haka ne bayanda shugabannin kasashen Faransa, Burtaniya da kuma Canada suka bukaci HKI ta dakatar da kissan kiyashi na gaza ta kuma bar kayakin agaji su shiga yankin idan ba haka ba suna iya daukar matakai masu tsauri a kanta. Badenoch  Shugaban jam’iyyar Conservative ya ce wannan bai wadatar ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Red Crescent ta Iran da Red Cross ta Saliyo sun cimma yarjejeniyoyi da dama a tsakaninsu
  • Araghchi: “Ba ma wasa game da batun inganta uranium, wanda hakkin al’ummar Iran ne”
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Yayi Tir Da Jakadan Burtaniya A Amurka Dangane Da Tashe Uranim A Kasar
  •  Arakci: Idan Birtaniya Ta Ci Gaba Da Batun Dakatar Da Tace Uranium A Iran, Za A Dakatar Da Tattaunawa Da Ita
  • Jagoran Juyin Juya Halin Musulunci Ya Ce: Dole Ne A  Dauki Kwararan Matakan Don Dakatar Da Laifukan Gaza
  • Tare Da Taimakon Kasar China Za A Bude Masana’antun  Sarrafa Sanadarin Lithium A Nigerria
  • Shugaban Jam’iyyar Adawa A Burtaniya Ya Ce HKI Tana Yaki A Gaza Ne A Madadin Gwamnatin Kasar
  • Iran Ta Kira Yi Jakadan Faransa Akan Furucin Ministan Harkokin Wajen Kasarsa
  • Sheikh Na’im Kassim: Gwagwarmaya Tana Da Wata Hanyar Ta Korar ‘Yan Mamaya