Kasar Uganda Ta Yanke Huldar Husoje Da Kasar Jamus Bayan Sabanin Diblomasiyya A Tsakaninsu
Published: 26th, May 2025 GMT
Kasar Uganda ta dakatar da aikin hadin giuwa na soje dake tsakanin kasashen biyu, saboda sukan da jakadan kasar Jamus yayiwa dan shugaban kasar yake kuma goyon bayan wata jam’iyyar adawar kasar.
Shafin yanar gizo na labarai Afirka News ya nakalto jami’iyyar shugaban kasar Uganda People’s Defence Forces (UPDF) tana bada rahoton cewa Jakada Schauer na kasar Jamus a Kamfani ya halarci wata taro tare da wata jam’iyyar adawa inda yake sukar dan shugaba Uwere Musevene jan yadda jam’iyyarsu take gudanar da harkokin shugabancin kasar.
Kasashen Uganda da Jamus sun dade basu sami irin wannan rashin jituwa ba. Kuma harkokon kasuwanci tsakanin kasashen biyu yakai dalar Amurka miliyon $335 a shekara 2023 kadai.
Sai dai muna iya cewa wannan ba zo da mamaki ba saboda shugaban yana shirin sake tsayawa takara a shekara 2026 mai zuwa.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnati Ta Taya Tinubu Murna Kan Goyon Bayan Da Ya Samu Don Komawa Takara
Daga Bello Wakili
Mataimaki na Musamman ga Shugaban Kasa kan Harkokin Yada Labarai da Ayyuka na Musamman, Mista Tunde Rahman, ya bayyana jerin goyon bayan da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ke samu daga cikin jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a matsayin shaida mai karfi kan tsare-tsaren da gwamnati ta aiwatar cikin shekaru biyu da suka gabata.
A yayin wata tattaunawa da ya yi da Radio Nigeria a Abuja, Mista Rahman ya ce goyon bayan da ke fitowa daga gwamnoni na APC, ‘yan majalisar dokoki da shugabannin jam’iyya, na nuna karuwar amincewa da sauye-sauyen tattalin arzikin da Shugaba Tinubu ya aiwatar. Ya ce wannan ya hada da cire tallafin fetur da daidaita farashin canjin kudade.
“Wadannan goyon bayan suna da matukar muhimmanci. Su ne jinjina ga jarumtaka da kwarin gwiwar Shugaban kasa, musamman wajen daukar matakai masu wahala tun farkon wa’adinsa, kamar cire tallafin man fetur a ranar 29 ga Mayu, 2023,” in ji shi.
A cewarsa, tasirin wadannan matakai ya fara haifar da sakamako mai kyau, ciki har da farfadowar tattalin arziki, saukin darajar Naira da kuma dan saukin farashin kayan abinci.
Ya kara da cewa shugabannin jam’iyya da mambobinta sun fahimci amfanin wadannan tsare-tsare, shi ya sa suke marawa Shugaban kasa baya.
Da aka tambaye shi ko wannan amincewar baiyi wuri ba alhali sauran kusan shekaru biyu kafin zabe, Mista Rahman ya ce hakan ba sabon abu ba ne a siyasar Najeriya, domin har jam’iyyun adawa sun riga sun fara shirin tunkarar zabe.
“Baiyi wuri ba. APC na mayar da martani ne ga abubuwan da ke faruwa a siyasa. Abin da ke faruwa yanzu wani nau’in tantancewa ce ta wa’adin gwamnati,” in ji shi.
Mista Rahman ya kuma ambaci sauya shekar gwamnan Jihar Delta zuwa APC tare da wasu daga cikin mambobin majalisar dokoki da masu rike da mukamai a gwamnatinsa a matsayin karin hujjar karuwar goyon bayan da Shugaba Tinubu ke samu.
Ya kammala da cewa a yi tsammanin karin goyon baya da sauya sheka daga gun wainda ba yan jamiyar APC ba nan gaba kadan yayin da gwamnatin ke ci gaba da nuna nasara da kwanciyar hankali a kasar.
BELLO WAKILI