Aminiya:
2025-06-01@16:31:14 GMT

Sojoji sun kashe ɗan ta’adda da aka sa ladar N100m a kansa a Bor

Published: 31st, May 2025 GMT

Sojojin Najeriya sun yi nasarar kashe wani kwamandan ’yan ta’adda, Amir Abu Fatima da aka sanya ladar Naira miliyan 100 ga duk wanda ya kama shi ko ya tona asirin inda yake, aka kama shi.

Sojoji sun halaka Abu Fatima ne a wani samame na musamman da suka kai a yankin Arewacin Jihar Borno.

Majiyar leken asiri ta sanar da Zagazola Makama cewa an kai harin ne da sanyin safiyar Juma’a, a yankin Kukawa da ke yankin Tafkin Chadi.

Majiyoyin soji sun tabbatarwa da Zagazola Makama cewa, wannan aikin wani shiri ne da aka tsara a tsanake na halaka ‘yan ta’adda da nufin kashe Abu Fatima, wani babban jigo na ‘yan tada kayar baya.

Dakaru na musamman sun kutsa cikin yankin da ‘yan ta’addan suke  inda suka yi artabu da su a wani kazamin musayar wuta.

Abu Fatima ya samu munanan raunuka yayin arangamar kuma an kama shi da rai sai dai daga bisani ya mutu sakamakon zubar da jini da ya wuce kima sakamakon harbin bindiga da ya samu a yakin.

Majiyarmu ta bayyana cewa an kashe babban kwamandan sa na biyu, masu hada bama-bamai, da wasu mayaka da dama a samamen.

Kayayyakin da aka ƙwato daga farmakin sun hada da bindigogi kirar AK-47 da dama, da akwatunan harsasai  masu yawa, da kayan ƙera bama-bamai, da sauran kayan yaƙi.

Abu Fatima dai ya kasance cikin jerin sunayen da jami’an tsaro ke nema ruwa a jallo saboda hannu a hare-haren ta’addanci da dama a yankin Tafkin Chadi.

Ana kallon mutuwarsa a matsayin wani babban koma baya na aiki da tunani ga cibiyoyin ’yan ta’adda da ke aiki a yankin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: yan ta adda yan ta adda

এছাড়াও পড়ুন:

Macron : Faransa za ta iya sanya takunkumi ga gwamnatin Isra’ila matukar ba ta kawo karshen killace Gaza ba

Shugaban na Faransa ya ce Faransa za ta iya sanya takunkumi ga gwamnatin Isra’ila matukar ba ta kawo karshen killace Gaza ba, inda kuma ya bukaci kasashen duniya da kada su jajirce wajen tunkarar matsalar karancin abinci a Gaza.

A wani taron manema labarai a Singapore a ranar Juma’a, Macron ya ce dole ne Turawa su “tsaurara matsayinsu na hadin gwiwa” kan Isra’ila, “idan babu wani mataki da ya dace da yanayin jin kai, a cikin sa’o’i da kwanaki masu zuwa” a zirin Gaza.

Macron ya ce, “Katange ayyukan jin kai yana haifar da yanayi mara kyau,” yayin taron manema labarai na hadin gwiwa tare da Firaministan Singapore Lawrence Wong.

Ya yi wadannan kalamai ne a daidai lokacin da gwamnatin Isra’ila ta kakaba wa Gaza takunkumin hana agajin jin kai na tsawon watanni kusan uku.

Isra’ila dai ta zargi Macron da kasancewa a cikin “yan tawaye” ga gwamnatin tel-Aviv bayan da shugaban Faransa ya ce dole ne kasashen Turai su tsaurara matakansu na hadin gwiwa kan Isra’ila idan har ba a dauki matakin jin kai ba.

Gwamnatin Isra’ila dai ta yi kunnen uwar shegu da kiraye-kirayen da kasashen duniya suka yi dangane da bala’in karancin abinci a Gaza, tana mai cewa ya ba da izinin kai kayan agajin a karkashin wani sabon tsarin hadin guiwa  da Amurka.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ma’aikatar Lafiyar Sudan Ta Ce: An Dan Samu Ja Da Baya A Cutar Kwalara Da Ta Kunno Kai A Kasar
  • Kungiyar Hamas Ta Bukaci Masu Shiga Tsakani Amurkawa Su Gamsar da Ita Za’a Dakatar Da Yaki A Gaza
  • ‘Yan Gwagwamayar Falasdinu Sun Halaka Sojojin Mamayar Isra’ila Masu Yawa A Wani Harin Kwanton Bauna
  • Sojoji sun cafke ɗan ta’adda sun ƙwato makamai a Filato
  • Macron : Faransa za ta iya sanya takunkumi ga gwamnatin Isra’ila matukar ba ta kawo karshen killace Gaza ba
  • MDD: Yankin Gaza Ne Ya Fi Ko’ina Fama Da Yunwa A Doron Kasa
  • Sojoji Sun Kashe Ƴan Ta’adda 60 A Borno
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Aiwatar Da Kisan Kiyashi Kan Falasdinawa A Yankin Zirin Gaza
  • Ana Fargabar Mutane Da Dama Sun Rasu Sakamakon Ambaliyar Ruwa A Neja