Aminiya:
2025-07-25@15:35:12 GMT

Sojoji sun kashe ɗan ta’adda da aka sa ladar N100m a kansa a Bor

Published: 31st, May 2025 GMT

Sojojin Najeriya sun yi nasarar kashe wani kwamandan ’yan ta’adda, Amir Abu Fatima da aka sanya ladar Naira miliyan 100 ga duk wanda ya kama shi ko ya tona asirin inda yake, aka kama shi.

Sojoji sun halaka Abu Fatima ne a wani samame na musamman da suka kai a yankin Arewacin Jihar Borno.

Majiyar leken asiri ta sanar da Zagazola Makama cewa an kai harin ne da sanyin safiyar Juma’a, a yankin Kukawa da ke yankin Tafkin Chadi.

Majiyoyin soji sun tabbatarwa da Zagazola Makama cewa, wannan aikin wani shiri ne da aka tsara a tsanake na halaka ‘yan ta’adda da nufin kashe Abu Fatima, wani babban jigo na ‘yan tada kayar baya.

Dakaru na musamman sun kutsa cikin yankin da ‘yan ta’addan suke  inda suka yi artabu da su a wani kazamin musayar wuta.

Abu Fatima ya samu munanan raunuka yayin arangamar kuma an kama shi da rai sai dai daga bisani ya mutu sakamakon zubar da jini da ya wuce kima sakamakon harbin bindiga da ya samu a yakin.

Majiyarmu ta bayyana cewa an kashe babban kwamandan sa na biyu, masu hada bama-bamai, da wasu mayaka da dama a samamen.

Kayayyakin da aka ƙwato daga farmakin sun hada da bindigogi kirar AK-47 da dama, da akwatunan harsasai  masu yawa, da kayan ƙera bama-bamai, da sauran kayan yaƙi.

Abu Fatima dai ya kasance cikin jerin sunayen da jami’an tsaro ke nema ruwa a jallo saboda hannu a hare-haren ta’addanci da dama a yankin Tafkin Chadi.

Ana kallon mutuwarsa a matsayin wani babban koma baya na aiki da tunani ga cibiyoyin ’yan ta’adda da ke aiki a yankin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: yan ta adda yan ta adda

এছাড়াও পড়ুন:

Ma’aikatar Harkokin Wajen Kasar Iran Ta Ce: Taro Tsakanin Iran Da Tawagar Kasashen Turai Dama Ce Ta Gyarar Tunanin Tarai

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran ya bayyana cewa: Taron Istanbul wata dama ce ta gyara matsayar Turai kan shirin makamashin nukiliyar Iran

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Isma’il Baqa’i, ya yi la’akari da taron na yau tsakanin Iran da kasashe uku mambobin kungiyar hadin gwiwa ta JCPOA a matsayin wata muhimmiyar dama ta gyara ra’ayoyinsu da gwada hakikaninsu kan batun makamashin nukiliyar kasar Iran.

A cikin wata sanarwa da ya aikewa kamfanin dillancin labaran IRNA, Isma’il Baqa’i ya bayyana fatansa na cewa wadannan kasashe uku za su yi amfani da wannan damar wajen gyara tsarin da suka bi a baya wanda bai dace ba, wanda ya lalata martabar Turai da matsayin tattaunawa, tare da mayar da ita a matsayin yar wasa maras tushe.

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar ya bayyana takaicinsa game da matsayin kasashen Turai uku na nuna son zuciya dangane da wuce gona da iri da gwamnatin ‘yan sahayoniyya da Amurka suka dauka kan kasar Iran – wadanda suka gabatar da wadannan kasashe uku ga duniya a matsayin tushe haifar da hargitsi da mara wa ta’addanci gindi. Ya ce: Jamhuriyar Musulunci ta Iran a baya ta yi zanga-zangar nuna rashin amincewa da irin wadannan matsayar da ba ta dace ba, kuma tabbas a taron na yau Juma’a za a isar da zanga-zangar Iran dangane da hakan ga bangarorin Turai, kuma za a bukaci su yi karin haske.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kai hari a ƙauyuka uku da kashe mutum 7 a Imo
  • Wasu Mahara Sun Sake Kashe Mutum 14 A Wani Kauyen Jihar Filato
  • An kashe mata da yara a sabon harin Filato
  • Bukatar Hukunta Masu Jagorantar Kashe-kashe A Nijeriya
  • Ma’aikatar Harkokin Wajen Kasar Iran Ta Ce: Taro Tsakanin Iran Da Tawagar Kasashen Turai Dama Ce Ta Gyarar Tunanin Tarai
  • Sojoji sun kashe ’yan ta’adda 95 a Neja, sun ceto mutum 138 da aka sace
  • Sojoji sun kashe Kwamandan Boko Haram Ibn Khalid a Borno
  • Sojoji Sun Kashe Kwamandan Boko Haram Ibn Khalid A Borno
  • Gwamna Sule Ya Ƙara Musanta Zargin Kare Ƴan Ta’adda A Nasarawa
  • Ɗan Shekaru 15 Ya Kashe Wani Matashi Kan Rikicin Gona A Jigawa