Aminiya:
2025-11-02@13:45:08 GMT

Sojoji sun kashe ɗan ta’adda da aka sa ladar N100m a kansa a Bor

Published: 31st, May 2025 GMT

Sojojin Najeriya sun yi nasarar kashe wani kwamandan ’yan ta’adda, Amir Abu Fatima da aka sanya ladar Naira miliyan 100 ga duk wanda ya kama shi ko ya tona asirin inda yake, aka kama shi.

Sojoji sun halaka Abu Fatima ne a wani samame na musamman da suka kai a yankin Arewacin Jihar Borno.

Majiyar leken asiri ta sanar da Zagazola Makama cewa an kai harin ne da sanyin safiyar Juma’a, a yankin Kukawa da ke yankin Tafkin Chadi.

Majiyoyin soji sun tabbatarwa da Zagazola Makama cewa, wannan aikin wani shiri ne da aka tsara a tsanake na halaka ‘yan ta’adda da nufin kashe Abu Fatima, wani babban jigo na ‘yan tada kayar baya.

Dakaru na musamman sun kutsa cikin yankin da ‘yan ta’addan suke  inda suka yi artabu da su a wani kazamin musayar wuta.

Abu Fatima ya samu munanan raunuka yayin arangamar kuma an kama shi da rai sai dai daga bisani ya mutu sakamakon zubar da jini da ya wuce kima sakamakon harbin bindiga da ya samu a yakin.

Majiyarmu ta bayyana cewa an kashe babban kwamandan sa na biyu, masu hada bama-bamai, da wasu mayaka da dama a samamen.

Kayayyakin da aka ƙwato daga farmakin sun hada da bindigogi kirar AK-47 da dama, da akwatunan harsasai  masu yawa, da kayan ƙera bama-bamai, da sauran kayan yaƙi.

Abu Fatima dai ya kasance cikin jerin sunayen da jami’an tsaro ke nema ruwa a jallo saboda hannu a hare-haren ta’addanci da dama a yankin Tafkin Chadi.

Ana kallon mutuwarsa a matsayin wani babban koma baya na aiki da tunani ga cibiyoyin ’yan ta’adda da ke aiki a yankin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: yan ta adda yan ta adda

এছাড়াও পড়ুন:

Borno ta fara fitar da kayan robobi zuwa ƙasashen waje – Zulum

Gwamnan Jihar Borno, Umara Zulum ya sanar da fara fitar da kayayyakin robobi zuwa ƙasashen duniya wanda hakan ke nuna wani gagarumin ci gaba a wani ɓangare na ƙoƙarin farfaɗo da tattalin arzikin Jihar.

Gwamnan ya jaddada cewa, wannan matakin wani ɓangare ne na babbar ajanda na bunƙasa masana’antu da kuma kawar da dogaro da jihar kan yi na kason da gwamnatin tarayya ke bayarwa duk wata.

Ƙwallo ta kashe ɗan wasan Cricket Za a rataye wanda ya kashe ɗan uwansa a Ekiti

Zulum ya sanar da hakan ne a ranar Alhamis yayin rangadin duba masana’antar robobi ta Borno da ke cikin yankin masana’antu na Maiduguri.

“Ina farin cikin lura cewa mutanen Jihar Borno ba za su sake sayen kayan robobi daga wasu wurare ba, kun ga an sayar da kayayyakin ga ƙasashen maƙwabta da sauran jihohi a cikin Najeriya.”

“Za mu zuba jari sosai a masana’antunmu, don haka nan gaba kaɗan, gwamnatin Jihar Borno ba za ta sake dogara da asusun tarayya ba don ayyukanta na yau da kullum,” in ji Zulum.

Gwamnan ya bayyana cewa masana’antar ta fara fitar da kayayyakinta ga ƙasashen waje, tare da jigilar kayayyakin filastik da aka gama zuwa ƙasashe maƙwabta kamar Chadi da Jamhuriyar Kamaru.

Zulum ya lura cewa an fara gina cibiyar ne a lokacin gwamnatin tsohon Gwamna Kashim Shettima, amma an farfaɗo da ita a matsayin wani ɓangare na shirin murmurewa da ci gaban gwamnatinsa.

Wasu daga cikin kayan robobin

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Wasu Yan Ta’adda Sun Kashe Dakarun Sa Kai 2 A Kudu Maso Gabashin Iran
  • Isra’ila Ta Kashe Mutane 4 Tare Da Jikkata Wasu Guda 3 A Kudancin Labanon
  • Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami
  • ‘An Kashe Masu Zanga-zanga Akalla 500 a Tanzania’
  • An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano
  • Sudan Ta Yi Kira Ga Kwamitin Tsaro Da Ya Ayyana RSF A Matsayin Kungiyar ‘Yan Ta’adda
  • Shugaban Lebanon Ya Umarci Sojoji Da Su Fuskanci Kutsen Na Isra’ila A Kudancin Kasar
  • Shugaban Lebanon Ya Umarci Sojoji Da Su Fuskanci Duk Wani Kutse Na Isra’ila A Kudancin Kasar
  • Borno ta fara fitar da kayan robobi zuwa ƙasashen waje – Zulum
  • Gaza: hare-haren Isra’ila sun kashe mutane 100 Cikin Kwanaki Biyu