Kafin tashinsa zuwa kasar Oman shugaban kasar Iran ya bayyana cewa: Suna neman kyakkyawar dangantaka da maƙwabtansu

Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian ya tabbatar kafin ya tashi daga filin tashi da saukar jiragen sama na birnin Tehran zuwa birnin Muscat a yammacin yau Talata cewa: Makasudin ziyarar tasa zuwa kasar Oman ita ce kulla kyakkyawar alaka da kasashe makwabta, kuma alaka tsakaninsu tana bunkasa kowace rana.

Shugaba Pezeshkian da yake zantawa da manema labarai a filin tashi da saukar jiragen sama na Mehrabad ya bayyana cewa: A halin yanzu yawan ciniki tsakanin Iran da Oman ya kai dalar Amurka biliyan 2.3, yana mai jaddada bukatar ci gaba da karfafa dangantakar dake tsakanin kasashen biyu.

Shugaba Pezeshkian ya ce: Zai gudanar da wannan ziyara ce bisa gayyatar da Sultan Haitham bin Tariq Al Said ya yi masa a hukumance, kuma bisa ga dukkanin manufofin gwamnati da Jagoran juyin juya halin Musulunci, manufar wannan ziyara ita ce kulla alaka mai zurfi da kyakykyawan dangantaka da kasashen makwabta ciki har da masarautar Oman, haka kuma an shirya fadada dangantakar Jamhuriyar Musulunci ta Iran a dukkanin bangarori na siyasa da tattalin arziki da zamantakewa.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Sin Ta Yi Kira Da A Karfafa Hadin Gwiwa A Fannin Tattalin Arziki Na Zamani

Mataimakin firaministan Sin Ding Xuexiang, ya yi kira a karfafa hadin gwiwa a bangaren tattalin arziki na zamanni ko kuma tattalin arziki na dijital.

Ding Xuexiang ya bayyana haka ne jiya Juma’a, yayin da ya halarci bikin bude taron kungiyar kasashen hadin kai ta Shanghai (SCO) kan tattalin arzikin dijital, a birnin Tianjin dake arewacin kasar Sin.

Cikin jawabinsa na bude taron, Ding Xuexiang wanda kuma mamba ne na kwamitin dindindin na ofishin siyasa na kwamitin kolin JKS, bisa la’akari da damarmaki da kalubale da na’urori da fasahohin zamani suka zo da su, ya kamata a yi kokarin gaggauta aiwatar da muhimmiyar matsayar da shugabannin kasashen SCO suka cimma da kuma yarjejeniyar tafiyar da harkokin fasahohin zamani ta duniya.

Mataimakin firaministan ya kuma bayar da shawarar inganta hadin gwiwa a bangaren tattalin arziki na dijital da karfafa manufofin tuntubar juna da tsara burinkan ci gaba na kasashen ta yadda za su dace da juna da yin cikakken amfani da dandamalin hadin gwiwa kamar na taron na SCO kan tattalin arzikin dijital, domin kara wa kokarin raya bangaren kuzari. (Mai fassara: Fa’iza Mustapha)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu ya dawo Najeriya bayan ziyarar aiki a Saint Lucia da Brazil
  • Sin Ta Yi Kira Da A Karfafa Hadin Gwiwa A Fannin Tattalin Arziki Na Zamani
  • Kyautar ‘Jakadan Abota’ Na Kasar China Ya Shiga hannun Iran
  • Lavrov: Shuwagabannin Kasashen Yammacin Turai Suna Son Shiga Yaki Da Rasha
  • Yadda aka kama ɗan bindiga ɗauke da N13m a hanyar Jos
  • Yadda aka kama ɗan bindiga ɗauke da N13m da bindigogi a hanyar Jos
  • Kamfanonin Jiragen Ruwa Sun Yanke Hulda Da Isra’ila Saboda Matsalar Hare-Haren Kasar Yemen
  • Shugaban Kasar Iran Yace Huldar kasar Iran Da IAEA Zai Ci Gaba Ne Idan Ta Daina Fuska Biyu
  • Zagaye na 5 A Tattaunawar Gaza da HKI  Ya tashi ba tare da Sun Dai-daita ba A Doha
  • Aragchi Ya Tattauna Da Bin Salman Kan Karfafa Zumunci Tsakanin Kasashen Biyu