HausaTv:
2025-05-27@19:17:09 GMT

An Sake Zaben Qalibof A Matsayin Shugaban Majalisar Dokokin Kasar Iran

Published: 27th, May 2025 GMT

Majalisar dokokin kasar Iran ta sake zaben Mohammad Baqir Qalibof a matsayin shugaban majalisar dokokin kasar na wata shekara a zaben da aka gudanar a cikin majalisar a jiya Litinin.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran,  ya bayyana cewa ya sami kuriu 219 daga cikin Jimillan kuri’u 272, wanda ya bashi babban rnjaye a kan sauran wadanda suke takara da shi.

Wannan kuma ya nuna cewa shugaban majalisar ya na da karbuwa a cikinta. Kuma yana da tasiri a cikin al-amuran gwamnati musamman a lokacinda kasar take fama da barazana a ciki da wajen kasar, musamman dangane da tattaunawa kan shirin makamashin Nukliyar kasar, wanda ake tattaunawa a kansa da Amurka.

An gudanar da wasu zabubbuka a cikin majalisar tare da fitar da yan majalisun da suka dace wajen rike su.

Akan gudanar da zabe don rike wasu mukamai a majalisar dokokin kasar Iran ne a ko wace shekara. Yan majalisa da dama sun bayyana gamsuwarsu da shugaban Qalibof na shekarar da ta gabata.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Ministan Gine-Ginen Hanyoyi Na Kasar Iran Tana Kasar Iraki Don Kula Da Aikin Layin Dogo

Ministan gina hanyoyi da ci gaban kasa na JMI Farzaneh Sadegh ta ziyarci kasar Iraki don bin duddugin aikin layin dogo da ake ginawa tsakanin kasashen biyu.

Farzaneh Sadegh ta isa bienin Bagdaza a jiya Asabar inda mataimakin ministan sifiri na kasar Iraki da kuma jakadan kasar Iran a Bagdaza suka yi maraba da ita.

Ministan ta ziyarci inda sojojin Amurka suka kashe kwamandojin yaki da yan  ta’adda Janar Kasim Sulaimani da kuma Mahdi Almuhandis a cikin watan Jenerun shekara ta 2020.

Farzaneh Sadegh zata gana da firai ministan kasar Iraki Mohammad shiaa Assudani, da wasu jami’an gwamnatin kasar Iraki. Sannan zata ziyarci aikin shimfida layin dogo mai tsawon kilomita 33 wadanda kasashen biyu suke yi don hada garin Chalamce da birnin Basra ba kasar Iran, wanda zai bawa miliyoyin yan kasar Iran ziyarar wurare masu tsarki a kasar Iraki a ranakun 40 na Imam Hussain (a).

Tun shekara ta 2014 ne kasashen biyu suka so kammala aikin amma yan ta’adda suka hana aikin tafiya. Sannan aka sabonta yarjeniyar a shekara ta 2023 wanda ake     saran aikin zai kammala kuma a fara aiki da layin dogon a Bana.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaban Kasar Iran Ya Kai Ziyara Zuwa Kasar Oman don Karfafa Kyakkyawar Alakar Kasashen Biyu
  • Rikici ya barke a taron Atiku da kungiyoyin Arewa
  • Iran Tana Gudanar Da Ayyukan Cibiyoyin Makamashin Nukiliyarta Bisa Maslahar Kasarta Ne
  • ‘Yar Majalisar Dokokin Ireland Ta Yi Suka Kan Shugabannin Turai Tare Da Neman Afuwa Daga Falasdinawa
  • Ministan Gine-Ginen Hanyoyi Na Kasar Iran Tana Kasar Iraki Don Kula Da Aikin Layin Dogo
  • An Gudanar da Zabukan Larduna A Kudancin Kasar Lebanin A Cikin Barazanar HKI
  • An Gargadi Shugaban Amurka Dangane Da Fadawa Iran Da Yaki
  • Shugaban Hukumar DSS Ya Kaddamar Da Cibiyar Koyar Da Addinin Musulunci A Kaduna 
  • Afirka Ta Kudu Ta Zargi Shugaban Kasar Amurka Da  Rashin Dalili Akan Zargin Yi Wa Fararen Fatar Kasar Kisan Kiyashi