Aminiya:
2025-11-02@20:55:56 GMT

Babu wanda ya tayar da bam a Abuja —Wike

Published: 29th, May 2025 GMT

Ministan Birnin Tarayya, Nyesom Wike ya ce rahotannin da ya samu na nuna babu gaskiya a labarin da ake yaɗawa cewa mai ƙunar baƙin wake ne ya tada abu mai fashewa a barikin soji na Mogadishu da ke Abuja.

Wike ya bayyana hakan ne ga manema labarai, lokacin da ya kai ziyarar duba aikin titunan da za a ƙaddamar domin bikin cikar shugaba Tinubu biyu a kan karagar mulki.

Sojoji sun halaka mayakan ISWAP da dama a Borno Bashin da ake bin Najeriya zai koma tiriliyan 162

Ministan ya kuma ja hankalin ’yan jarida kan yaɗa labaran da ka iya jefa firgici a zuƙatan al’umma.

Aminiya ta rawaito cewa lamarin ya faru ne a shingen bincike na barikin sojin Mogadishu, kuma hukumar bada agajin gaggawa ta kasa (NEMA) ce a ranar Talata ta ce harin ɗan ƙunar baƙin wake ne.

“Jami’an tsaro ba su ce harin ɗan ƙunar baƙin wake ba ne. Saboda haka kar ku je kuna tsorata mutane da maganganu marasa tushe. Ku dinga binciken ƙwaƙwaf kafin yaɗa labaranku. NEMA ba shugabar tsaro ba ce,  ma’aikatun tsaro na wurin.

“Abin da ya faru shi ne wani ne ya je wuraren da muke fasa dutsuna. Sai ya ɗauki nakiyar da ake fasa dutse ya saka a aljihu wataƙila don bai san illar hakan ba. Shi ne ta fashe a jikinsa. Ka ga ai hakan ba yana nufin ɗan ƙunar baƙin wake ba ne,” in ji ministan.

Sai dai ya zuwa lokacin haɗa rahoton, daga rundunar soji har ta ’yan sanda, babu wacce ta ce komai kan hakan, sun dai ce suna gudanar da bincike.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: kunar bakin wake Tsaro ƙunar baƙin wake

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Yobe ta ƙaddamar da shirin amfani da ma’adanai

Gwamnatin Jihar Yobe ta ƙaddamar da shirin fara amfani da ma’adinan ƙarƙashin ƙasa da Allah SWT ya hore ma ta da nufin haɓaka tattalin arzikinta tare da samarwa al’umma aikin yi.

A yayin ƙaddamar da taron masu ruwa da tsaki na Jihar da aka yi a babban ɗakin taron gidan gwamnatin Jihar da ke Damaturu, Gwamnan Jihar Mai Mala Buni ya ce kamfanin haɓaka ma’adanai ta Yobe Limited ita ce kawai hukumar da aka bai wa izini don gudanar da duk ayyukan bincike da haƙar ma’adinai a faɗin jihar.

Kotu ta dakatar da babban taron PDP na ƙasa Real Madrid zata nemi diyyar Dala bilyan 4 daga UEFA

Yana mai cewa, kamfanin haƙar ma’adinai na Yobe a halin yanzu shi ne, ƙashin bayan da zai samarwa Jihar hanyoyin dogaro.

“Jihar Yobe tana da wadataccen albarkatun ma’adinai kamar: Limestone, gypsum, kaolin, granite, Quartz, silica da sauran su duk da haka, tsawon shekaru da yawa, waɗannan ma’adinai sun kasance ba a amfani da su sosai kuma a yanzu lokaci ya yi da za a mayar da waɗannan ma’adinai da aka ɓoye zuwa kadarorin da za su samar da ayyukan yi, samar da wadata da kuma ciyar da ci gaban zamantakewa da tattalin arziki na mutanenmu gaba ɗaya.”

“Manufarmu ita ce tsara wani tsari don ci gaban fannin haƙar ma’adinai a Jihar Yobe ta hanyar da ta dace da manufofin Gwamnatin Tarayya na tabbatar da haɗa kan al’umma, jawo hankalin masu zuba jari masu aminci da kuma tabbatar da alhakin gyara muhalli.

“kuma mun yi imanin cewa haƙar ma’adinai idan aka sarrafa shi yadda ya kamata, zai iya zama babban abin da ke haifar da juriyar tattalin arzikin jiharmu, samar da aikin yi ga matasa da kuma samar da kuɗaɗen shiga.”

“Muna hasashen samar da fannin haƙar ma’adinai wanda zai iya aiki a cikin tsarin dokoki, wanda ke tabbatar da ɗorewar muhalli da fa’idar al’umma; wanda ke haɗaka da haɗin gwiwar gwamnati da masu zaman kansu waɗanda aka amince da riƙon amana; wanda ke jawo hankalin masu zuba jari na ƙasashen waje.” Cewar Gwamna Buni.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tsaro: Taimakonmu Amurka ya kamata ta yi maimakon barazana — Kwankwaso
  • Tsaro: Taimakonmu Amurka ya kamata ta yi maimakon ba barazana ba — Kwankwaso
  • IAEA : Babu wata shaida da ke nuna cewa Iran na kera makaman nukiliya
  • Rikicin PDP: Tsagin Wike ya dakatar da Damagum
  • PDP ta dakatar da Anyanwu da wasu ’yan tsagin Wike
  • PDP ta dakatar da Anyanwu da wasu da ke da alaƙa da Wike
  • Barcelona ta shiga zarwacin Victor Osimhen
  • Gwamnatin Yobe ta ƙaddamar da shirin amfani da ma’adanai
  • Matsalar Tsaro: Ko Sabbin Shugabannin Rundunar Soji Za Su Kawo Sauyi?
  • Ana zargin ɗa da kashe mahaifinsa a Kano saboda hana shi ƙara aure