Aminiya:
2025-07-23@22:59:03 GMT

Babu wanda ya tayar da bam a Abuja —Wike

Published: 29th, May 2025 GMT

Ministan Birnin Tarayya, Nyesom Wike ya ce rahotannin da ya samu na nuna babu gaskiya a labarin da ake yaɗawa cewa mai ƙunar baƙin wake ne ya tada abu mai fashewa a barikin soji na Mogadishu da ke Abuja.

Wike ya bayyana hakan ne ga manema labarai, lokacin da ya kai ziyarar duba aikin titunan da za a ƙaddamar domin bikin cikar shugaba Tinubu biyu a kan karagar mulki.

Sojoji sun halaka mayakan ISWAP da dama a Borno Bashin da ake bin Najeriya zai koma tiriliyan 162

Ministan ya kuma ja hankalin ’yan jarida kan yaɗa labaran da ka iya jefa firgici a zuƙatan al’umma.

Aminiya ta rawaito cewa lamarin ya faru ne a shingen bincike na barikin sojin Mogadishu, kuma hukumar bada agajin gaggawa ta kasa (NEMA) ce a ranar Talata ta ce harin ɗan ƙunar baƙin wake ne.

“Jami’an tsaro ba su ce harin ɗan ƙunar baƙin wake ba ne. Saboda haka kar ku je kuna tsorata mutane da maganganu marasa tushe. Ku dinga binciken ƙwaƙwaf kafin yaɗa labaranku. NEMA ba shugabar tsaro ba ce,  ma’aikatun tsaro na wurin.

“Abin da ya faru shi ne wani ne ya je wuraren da muke fasa dutsuna. Sai ya ɗauki nakiyar da ake fasa dutse ya saka a aljihu wataƙila don bai san illar hakan ba. Shi ne ta fashe a jikinsa. Ka ga ai hakan ba yana nufin ɗan ƙunar baƙin wake ba ne,” in ji ministan.

Sai dai ya zuwa lokacin haɗa rahoton, daga rundunar soji har ta ’yan sanda, babu wacce ta ce komai kan hakan, sun dai ce suna gudanar da bincike.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: kunar bakin wake Tsaro ƙunar baƙin wake

এছাড়াও পড়ুন:

Jami’an tsaro sun dakile yunkurin Sanata Natasha na shiga harabar Majalisa

Jami’an tsaro sun hana Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan da ’yan rakiyarta shiga haramar Majalisar Dokoki ta Kasa, inda ta je da niyyar halartar zaman Majlasiar Dattawa a ranar Talata.

Jami’an tsaro a daukacin kofofin shiga harabar majalisar sun hana ta shiga harabar majalisar ne a lokacin da ta yi yunkurin shiga domin halartar zaman ranar Talata, a yayin da magoya bayanta suka rako ta domin nuna goyon bayansu gare ta kan dakatarwar da majalisar ta yi mata.

A watan Maris ne da Majalisar Dattawa ta dakatar da Sanata Natasha na tsawon wata shida kan zargin rashin da’a da kuma rashin bin tsarin wurin zaman da aka tanadar da mambobin majalisar a ranar 20 ga watan Fabrairu, 2025.

A kana haka ne ’yar majalisar mai wakiltar Kogit ta Tsakiya ta garzaya Babbar Kotun Abuja, wadda ta umarci majalidar ta dawo da Sanata Natasha, bisa hujjar cewa majailsar ta wuce gona da iri wajen dakatar da ita har na tsawon wata shida.

Kamfanonin lantarki za su katse wuta kan bashin N5.2trn da suke bin gwamnati  An wajabta wa ɗaliban firamare mallakar lambar NIN a Bauchi

Alkalin kotu, Mai Shari’a Binta Nyako, ya bayyana cewa hukuncin da majalisar ta yanke ya yi tsauri da yawa, kuma ba shi da mazauni a doka.

Ta bayyana cewa doka na bukatar majalisar ta zauna sau 181 ne a shekara, kuma dakatarwar ta kusa tsawon wadanan kwanaki.

Ta ce hakan na nufin al’ummarta za su shafe kusan shekara guda ba tare mai wakiltans su ba a zauren majalisar, kuma ya saba da dokar kasa.

Tun loakcin Natasha ke ta kokarin komawa bakin aiki, inda a ranar Asabar ta lashi takobin halartar zama a ranar Talatar nan, idan majalisar ta dawo daga hutu.

Amma a ranar Litinin Shguaban Kwamitin Sadarwa na Majalisar Dattawa, Sanata Yemi Adaramodu ya fitar da sanarwa yana gargadin ta da cewa ya nisanci majalsiar.

Adaramodu ya yi ikirarin cewa Natasha ba ta cika umarnin kotu na biyan tarar Naira miliyan biyar ga Gwamnatin Tarayya kan kan raina kotu ba, da kuwa wallafa sakon neman afuwa a manyan jaridu biyu da kuma shafinta na Facebook.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Kaddamar Da Bikin BIRTV2025 A Beijing
  • Tinubu na amfani da ƙarfin mulki wajen tsoratar da ’yan adawa — Sule Lamido
  • Babban Hafsan Sojin Iran Ya Ce: Iran Zata Sanya Duk Wanda Ya Dauki Matakin Wuce Gona Kanta Nadama
  • Har Yanzu Yaƙi Da Ta’addanci Ne Babban Muradin Gwamnatina — Tinubu
  • Trump ya fitar da Amurka daga UNESCO saboda amincewa da  Falasdinu a matsayin Mamba
  • Jami’an tsaro sun dakile yunkurin Sanata Natasha na shiga harabar Majalisa
  • Natasha Ta Koma Majalisar Dattawa Duk Da Tsaurara Tsaro
  • Gwamnatin Zamfara Ta Kira Babban Taron Tsaro Tare Da Bayyana Sabbin Dabaru Na Yakar ‘Yan Bindiga.
  • Libya Ta Tasa Keyar Baƙin Haure Yan Kasar Sudan 700 Zuwa Kasarsu
  • Ministocin Tsaron kasashen Rasha Da JMI Sun Hadu A Birnin Mosco