Babu wanda ya tayar da bam a Abuja —Wike
Published: 29th, May 2025 GMT
Ministan Birnin Tarayya, Nyesom Wike ya ce rahotannin da ya samu na nuna babu gaskiya a labarin da ake yaɗawa cewa mai ƙunar baƙin wake ne ya tada abu mai fashewa a barikin soji na Mogadishu da ke Abuja.
Wike ya bayyana hakan ne ga manema labarai, lokacin da ya kai ziyarar duba aikin titunan da za a ƙaddamar domin bikin cikar shugaba Tinubu biyu a kan karagar mulki.
Ministan ya kuma ja hankalin ’yan jarida kan yaɗa labaran da ka iya jefa firgici a zuƙatan al’umma.
Aminiya ta rawaito cewa lamarin ya faru ne a shingen bincike na barikin sojin Mogadishu, kuma hukumar bada agajin gaggawa ta kasa (NEMA) ce a ranar Talata ta ce harin ɗan ƙunar baƙin wake ne.
“Jami’an tsaro ba su ce harin ɗan ƙunar baƙin wake ba ne. Saboda haka kar ku je kuna tsorata mutane da maganganu marasa tushe. Ku dinga binciken ƙwaƙwaf kafin yaɗa labaranku. NEMA ba shugabar tsaro ba ce, ma’aikatun tsaro na wurin.
“Abin da ya faru shi ne wani ne ya je wuraren da muke fasa dutsuna. Sai ya ɗauki nakiyar da ake fasa dutse ya saka a aljihu wataƙila don bai san illar hakan ba. Shi ne ta fashe a jikinsa. Ka ga ai hakan ba yana nufin ɗan ƙunar baƙin wake ba ne,” in ji ministan.
Sai dai ya zuwa lokacin haɗa rahoton, daga rundunar soji har ta ’yan sanda, babu wacce ta ce komai kan hakan, sun dai ce suna gudanar da bincike.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: kunar bakin wake Tsaro ƙunar baƙin wake
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Kano za ta sabunta masallacin da aka kona masallata 23 a kan N150m
Gwamnatin Jihar Kano ta amince da kashe Naira miliyan dari da hamsin da ɗaya da dubu dari takwas da sittin da uku (N151,863,895.97) domin sake gina wani masallaci da wani matashi ya cinna wa wuta a yayin da jama’a ke tsaka da sallar Asuba a cikin jam’i a Tiga Gadan da ke Karamar Hukumar Gezawa, a watan Mayun bara.
Aikin sabunta masallacin ya kunshi gina makarantar Islamiyya tare da ofis da bandaki da kuma rijiyar burtsatse mai amfani da hasken rana tare da tankin ruwa na sama.
Kwamishinan Yada Labarai da Harkokin Cikin Gida na Jihar Kano, Ibrahim Abdullahi Wayya, ya sanar amincewar sake gina masallacin ya biyo bayan alkawarin da Gwamna Abba Kabir ya yi a lokacin da ya ziyarci wurin da abin ya faru.
Ya yi kira ga mutanen kauyen Gadan da su saka wannan karimci ta hanyar bayar da goyon bayan da ake bukata don tabbatar da nasarar kammala aikin, da kuma samar da kariya ga sabbin gine-ginen.
Yadda kotu ta yanke wa wanda ya kona mutane a cikin masallaci hukuncin rataya a Kano Amarya ta kashe uwargida da wuka a Katsina An yanke wa wanda ya yi wa agolarsa fyaɗe ɗaurin rai-da-raiA ranar Litinin ne Babbar Kotun Musukunci ta yanke wa Shafi’u Abubakar hukuncin kisa ta hanyar rataya saboda kona masallacin, wanda ya yi sanadin mutuwar mutane 23.