Fiye Da Falasdinawa 60 Ne Su Ka Yi Shahada A Jiya Laraba
Published: 29th, May 2025 GMT
A ci gaba da tafka laifukan yakin da HKI take yi a Gaza,Fiye da Falasdinawa 60 ne su ka yi shahada a jiya Laraba.
A wani harin da sojojin mamayar su ka kai a yankin Jabaliya, Falasdinawa 5 sun yi shahada, yayin da wani adadi mai yawa su ka jikkata.
Wani jirgin sama maras matuki ya kai wani harin a unguwar “Shuja’iyya” wnada ya yi sanadin shahadar mutum daya, sai kuma wasu shahidan 4 a unguwar “Shari’u 5”, da kuma wasu shahidan 4 a garin “Bani-Suhaila”.
Wasu rahotannin sun ce, ‘yan sahayoniyar sun kai wasu hare-haren a garin ‘Abasan al-kabira’ da ya yi sanadin shahadar mutum daya da kuma jikkatar wasu masu yawa.
A yankin Qizan kuwa, ‘yan sahayoniyar sun kai hari akan mutanen da suke kokarin isa wurin da za su sami kayan agaji, tare da kashe 5 daga cikinsu a yankin kudu maso yammancin garin Khan-Yunus.
Ita kuwa hukumar yankin na Gaza ta sanar da cewa; ‘yan sahayoniyar sun kashe fararen hula 10 wadanda yunwa ci karfinsu, sannan kuma ta jikkata wasu 62 a wurin da aka ware na raba kayan agaji.
Sanarwar ta hukumar Gaza ta kuma ce; Yankunan da aka ware domin raba kayan agaji a karkashin Amurka da Isra’ila’ ya zama tarkon da ake kashe mutane a wurin.
A gefe daya ma’aikatar kiwon lafiya ta Gaza ta sanar da cewa; Sojojin mamaya sun kai wa asibitin tafi da gidanka na “Red-Cross” hari dake “Mawasi, a gundunar Khan-Yunus. “Yan mamayar sun kai harin ne adaidai lokacin da ake yi wa wadanda su ka jikkata magani.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Kwamitin bincike na MDD ya zargi Isra’ila da aikata “kisan kare dangi” a Gaza
Kwamitin bincike mai zaman kansa na Majalisar Dinkin Duniya, ya fitar da wani rahoto mai zargin Isra’ila da laifin aikata kisan kiyashi a zirin Gaza.
A cikin sabon rahoto da ta gabatar a ranar Talata, MDD ta zargi shugaban kasar Isra’ila Isaac Herzog, da firaministan kasar Benjamin Netanyahu, da kuma tsohon ministan tsaro Yoav Gallant da “kimsa kisan kiyashi.”.
Rahoton ya tattara batutuwan da suka shafi farar hula kai tsaye, ciki har da yara, ya kuma bayyana cewa kisan kiyashin da ake yi ya fi yawa fiye da yadda aka yi tashe-tashen hankula a baya.
Masu binciken sun kuma tabbatar da cewa da gangan Isra’ila ta haifar da yanayin da ke barazana ga rayuwar Falasdinawa ta hanyar toshe hanyoyin samun muhimman kayayyaki na wannan al’umma.
Rahoton ya biyo bayan wani bincike da aka yi na tsawon shekaru biyu, kuma ya yi nuni da yadda ayyukan Isra’ila ke a matsayin kisan kare dangi.
A martanin da ta mayar, Isra’ila ta yi watsi da sakamakon binciken da cewa “karya ce “, ta kuma bukaci da a rusa hukumar nan take.
A sa’i daya kuma, kwamitin bincike na MDD ya yi kira ga kasashe da su daina baiwa Isra’ila makamai da kayan aikin da za a iya amfani da su wajen aikata kisan kare dangi.
Fitar da rahoton na zuwa ne mako guda gabanin babban taron Majalisar Dinkin Duniya a birnin New York, inda ake sa ran kasashe da dama za su amince da kasar Falasdinu a hukumance.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Iran da Saudiyya sun bukaci hadin Musulmi game da halin da ake ci a yankin September 17, 2025 Duniya na tir da sabon farmakin Isra’ila kan Gaza September 17, 2025 Akalla Falasdinawa 78 ne sukayi shahada a hare-haren Isra’ila a Gaza September 17, 2025 Akalla Falsdinawa 78 Ne Suka Yi Shahada A Yau A Gaza. September 16, 2025 Isra’ila Ta Kai Hari A Tashar Jirgin Ruwan Hudaida Dake Yamen September 16, 2025 Iran Ta Gabatar Da Sabbin Kayayyaki 5 A Wajen Taron kere-kere . September 16, 2025 Iran Ta Bukaci IAEA Tayi Tir Da Harin Da Isra’ila Ta Kai A Tashoshin Nukiyarta. September 16, 2025 Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana September 16, 2025 Pezeshkian: Saudiyya Na Iya Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Samar Da Hadin Kan Kasashen Musulmi September 16, 2025 Pezeshkian: Ta’addancin Haramtacciyar Kasar Isra’ila Kan Kasar Qatar Zalunci Ne Ga Diflomasiyya September 16, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci