HausaTv:
2025-06-05@01:53:59 GMT

 Fiye Da Falasdinawa 60 Ne Su Ka Yi Shahada A Jiya Laraba

Published: 29th, May 2025 GMT

A ci gaba da tafka laifukan yakin da HKI take yi a Gaza,Fiye da Falasdinawa 60 ne su ka yi shahada a jiya Laraba.

A wani harin da sojojin mamayar su ka kai a yankin Jabaliya, Falasdinawa 5 sun yi shahada, yayin da wani adadi mai yawa su ka jikkata.

Wani jirgin sama maras matuki ya kai wani harin a unguwar “Shuja’iyya” wnada ya yi sanadin shahadar mutum daya, sai kuma wasu shahidan 4 a unguwar “Shari’u 5”, da kuma wasu shahidan 4 a garin “Bani-Suhaila”.

Wasu rahotannin sun ce, ‘yan sahayoniyar sun kai wasu hare-haren a garin ‘Abasan al-kabira’ da ya yi sanadin shahadar mutum daya da kuma jikkatar wasu masu yawa.

A yankin Qizan kuwa, ‘yan sahayoniyar sun kai hari akan mutanen da suke kokarin isa wurin da za su sami kayan agaji, tare da kashe 5 daga cikinsu a yankin kudu maso yammancin garin Khan-Yunus.

Ita kuwa hukumar yankin na Gaza ta sanar da cewa; ‘yan sahayoniyar sun kashe fararen hula 10 wadanda yunwa ci karfinsu, sannan kuma ta jikkata wasu 62 a wurin da aka ware na raba kayan agaji.

Sanarwar ta hukumar Gaza ta kuma ce; Yankunan da aka ware domin raba kayan agaji a karkashin Amurka da Isra’ila’ ya zama tarkon da ake kashe mutane a wurin.

A gefe daya ma’aikatar kiwon lafiya ta Gaza ta sanar da cewa; Sojojin mamaya sun kai wa asibitin tafi da gidanka na  “Red-Cross” hari dake “Mawasi, a gundunar Khan-Yunus. “Yan mamayar sun kai harin ne adaidai lokacin da ake yi wa wadanda su ka jikkata magani.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Ambaliyar Mokwa: Yawan mutanen da suka salwanta ya haura 700

Iftila’in ambaliyar ruwa a garin Mokwa a Ƙaramar Hukumar Mokwa ta Jihar Neja ta yi ajalin mutane sama da 200, yayin da wasu sama da 500 suka bata.

Ambaliyar, wadda ita ce mafi muni a yankin cikin shekaru 60, ta shafi yankunan Tiffin Maza da Anguwan Hausawa, bayan ruwan sama kamar da bakin ƙwarya a ranar Laraba da ta gabata da daddare.

Ɗaruruwan gidaje sun lalace, inda mutane da yawa suka rasa matsugunansu.

Kafar yaɗa Labarai ta BBC ta ruwaito a ranar Litinin cewa yawan mutanen da suka mutu ya ƙaru zuwa sama da 200, kuma an dakatar da ayyukan ceto saboda hukumomi sun yanke ƙauna daga samun wasu da rai.

Babbar Sallah: Farashin kayan miya ya yi tashin gwauron zabo Yadda magidanci ya kuɓuta bayan wata 7 a hannun ’yan bindiga

Mata da ƙananan yara na daga cikin waɗanda ambaliyar ta rutsa da su, ciki har da almajirai masu yawan gaske a makarantun tsangaya a yankin.

Musa Kimboku, wani jami’in yankin, ya tabbatar da dakatar da ayyukan ceto. Hakimin Mokwa, Muhammadu Aliyu, ya bayyana cewa ba a iya haƙo wasu gawarwaki ba saboda sun shiga “ta Kogin Neja.”

Basaraken ya ƙara da cewa za a fara tono gawarwakin da suka maƙale a karkashin ƙasa domin hana yaduwar cututtuka.

Wani magidanci da ya rasa matarsa da jaririnsu a ambaliyar, Malam Adamu Yusuf, ya ba da labari: “Ina kallo amma babu abin sa zan iya na taimako yayin da ruwa ya share iyalina. Na tsira saboda ina iya yin iyo.”

Saliu Sulaiman, wani mazaunin yankin, yace ya rasa kusan $1,500 – kudin da ya samu daga sayar da kayan gonarsa – kuma ya rasa matsuguninsa.

Mazauna yankin suna zargin cewa fashewar wani madatsar ruwa da ke kusa ta ba da gudummawa ga tsananin ambaliyar ruwa, wanda har yanzu hukumomi ba su tabbatar da hakan ba.

Karfin ruwan ambaliyar ya kasance mai tsanani har ma an ga gawarwaki a garin Rabba, wanda ke da nisan tafiyar awa daya daga Mokwa.

Musa Kimboku na Karamar Hukumar Mokwa ya umurci kauyukan da ke makwabta da su binne “duk wata gawa da suka samu.”

Kamfanin Dillancin Labarai na Faransa (AFP) ya ruwaito wani masunci na yankin Danjuma Shaba, wanda ya rasa gidansa na cewa, “Ba ni da wurin kwana. Gidana ya riga ya rushe.”

Farida Auwalu, wacce ita kadai ce ta tsira da cikin ’yan uwanta 16, ta rasa ’ya’yanta bakwai a ambaliyar. An gano gawarwakin huɗu daga cikin yara an binne su.

“Fatana shi ne in ga sauran gawarwaki kuma in yi musu jana’izar da ta dace don samun nutsuwa,” in ji ta.

Waɗanda suka tsira daga ambaliyar ruwa suna ƙoƙarin samun taimakon farko.

Hassan Umar, wani mazaunin yankin, ya shaida wa Al Jazeera cewa waɗanda abin ya shafa ba su da kuɗi ko abinci, inda akasarinsu ke kwana a fili.

Ambaliyar ta haddasa rugujewar gadar da ta haɗa yankunan Koshaba da Rabba, kimanin kilomita 7 daga garin Mokwa, inda ruwan ambaliyar ya hadu da Kogin Neja, inda aka gano gawarwaki da yawa a wurin da ruwan ya hadu da kogin.

Alhaji Tanko Bala, shugaban al’ummar Hausawa a Mokwa, ya bayyana a karshen mako cewa mafi yawan waɗanda abin ya shafa suna kwana a fili saboda babu ingantattun tanadi daga gwamnati don samar musu da matsuguni.

Ya soki sansanin da aka keɓe a makarantar firamare a matsayin wanda ba za a iya zama a ciki ba kuma ba shi da kayan bukatun yau da kullum, yana mai kira ga gwamnati da ta taimaka wa wadanda abin ya shafa da kayan kwanciya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojojin HKI Suna Ci Gaba Da Kashe Falasdinawa Wadanda Suke Jin Yunwa A Gaza
  • Jami’an DSS sun kashe ’yan bindiga 45 a Neja
  • DAGA LARABA: Dalilan Tashin Farashin Kayan Miya Gabanin Bikin Sallah
  • Guardian: Isra’ila Tana Kai Wa Makarantun Dake Dauke Da ‘Yan Gudun Hijira a gaza Hari, Tana Sane Da Hakan
  • Ambaliyar Mokwa: Yawan mutanen da suka salwanta ya haura 700
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Aiwatar Da Wani Kisan Kiyashi Kan Masu Bukatar Kayan Agaji
  • Jiragen Yakin NAF Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 20, ‘Yan Banga 2 A Zamfara
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Kai Hari kan Falasdinawa Masu Karban Agajin Jin Kai A Rafah
  • Saudiyya : Matakin Isra’ila na hana mu ziyaratar falasdinwa, watsi ne da tayin zaman lafiya
  • Gaza : Sabon kisan kiyashi a kusa da wurin rarraba kayan abinci