Kwanan baya, a yayin da ake gudanar da taron kolin ASEAN karo na 46, wasu jami’an diplomasiya na kasar Philippines sun yi shelar daddale wasu yarjejeniyoyi tare da kasar Sin don kiyaye zaman lafiya a tekun kudancin kasar Sin. Duk da haka Philippines ta rika daukar matakan takala a zahiri. Kuma abun da kasar ta Philippines ta yi ya saba da ma’anar zaman lafiya.

Bayan da gwamnatin Marcos ta zartas da shirin doka na wai dangane da tekun kudancin kasar Sin daga bara zuwa yanzu, ta kasance a matsayin dillaliyar Amurka da wasu kasashen da ba su cikin yankin. Ta dauki matakan kashi kai don tada zaune tsaye a tekun kudancin kasar Sin da kirkira labarun shafa wa kasar Sin kashin kaji, ta kuma yunkura don tabbatar da hukuncin da aka yanke ba bisa doka ba game da tekun kudancin kasar Sin, ta hanyar kafa dokokin cikin gida. Amma a karshe dai ba ta cimma burinta na sake mulkin tsibirin Huangyan da sauran tsibiran Zhongsha ba, haka kuma ba ta cimma burinta na mamaye sashen tudun teku na Xianbin Jiao da na Tiexian Jiao da na Ren’ai Jiao karkashin inuwar tsibiran Nansha, inda babu wani dan Adam da ke da zama a wuraren.

Yau mako guda da ta wuce, kasar Sin da kungiyar ASEAN sun kammala tattaunawa kan yankin ciniki cikin ’yanci karo na 3, lamarin da ya samar da sabuwar dama wajen raya yankin. A daidai wannan muhimmin lokaci, Philippines ta yi takala da yunkurin danne kasar Sin bisa taimakon Amurka, kuma abin da ta yi bai dace da fatan al’ummar Philippines ba, kana ba zai samu goyon baya daga sauran kasashen da ke tekun kudancin kasar Sin ba, kana ba ya tafiya tare da kokarin yankin na samun zaman lafiya da ci gaba. A karshe dai, Philippines ba za ta samu kome ba sai dai salwantar da kanta cikin takarar da Amurka da sauran manyan kasashe suke yi. (Tasallah Yuan)

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: a tekun kudancin kasar Sin

এছাড়াও পড়ুন:

An Sake Zaben Qalibof A Matsayin Shugaban Majalisar Dokokin Kasar Iran

Majalisar dokokin kasar Iran ta sake zaben Mohammad Baqir Qalibof a matsayin shugaban majalisar dokokin kasar na wata shekara a zaben da aka gudanar a cikin majalisar a jiya Litinin.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran,  ya bayyana cewa ya sami kuriu 219 daga cikin Jimillan kuri’u 272, wanda ya bashi babban rnjaye a kan sauran wadanda suke takara da shi. Wannan kuma ya nuna cewa shugaban majalisar ya na da karbuwa a cikinta. Kuma yana da tasiri a cikin al-amuran gwamnati musamman a lokacinda kasar take fama da barazana a ciki da wajen kasar, musamman dangane da tattaunawa kan shirin makamashin Nukliyar kasar, wanda ake tattaunawa a kansa da Amurka.

An gudanar da wasu zabubbuka a cikin majalisar tare da fitar da yan majalisun da suka dace wajen rike su.

Akan gudanar da zabe don rike wasu mukamai a majalisar dokokin kasar Iran ne a ko wace shekara. Yan majalisa da dama sun bayyana gamsuwarsu da shugaban Qalibof na shekarar da ta gabata.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Falasdinawa 23 Suka Yi Shahada A Farmakin Da Sojojin Mamayar Isra’ila Suka Kai Kan Sansanin Al-Bureij
  • Sin Da Kasashen Yankin Pasifik Sun Yi Nasarar Gudanar Da Taron Ministocin Harkokin Wajen Karo Na Uku
  • Duniyarmu A Yau: Wasikar Lawyoyi 800 Ga Firay Ministan Kasar Burtaniya Kan Gaza
  •  Kasar Chile Na Shirin Yanke Alakar Diplomasiyya Da “Isra’ila”
  • Hadin Gwiwar Sin Da Yankin Turai Na Kara Kawo Haske Ga Tattalin Arzikin Duniya
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Yayi Tir Da Jakadan Burtaniya A Amurka Dangane Da Tashe Uranim A Kasar
  • Shugaban Kasar Iran Ya Kai Ziyara Zuwa Kasar Oman don Karfafa Kyakkyawar Alakar Kasashen Biyu
  • An Sake Zaben Qalibof A Matsayin Shugaban Majalisar Dokokin Kasar Iran
  • Tare Da Taimakon Kasar China Za A Bude Masana’antun  Sarrafa Sanadarin Lithium A Nigerria