Yemen: Wuce Gona Da Irin HKI Ba Zai Sauya Mana Ra’ayi Akan Ci Gaba Da Taimaka Wa Gaza Ba
Published: 29th, May 2025 GMT
Shugaban kungiyar Ansarullah ta kasar Yemen Sayyid Abdulmalik al-Husi ya bayyana cewa; Harin da “Isra’ila” ta kai wa filin saukar jiragen saman Sanaa, manufarsa ita ce yin matsin lamba akan matsayarmu ta taimakawa al’ummar Falasdinu da ake zalunta.”
Sayyid Abdulmalik al-Husi ya kara da cewa; Komai girman hare-haren da Isra’ilan za ta kai ba zai yi tasiri akan matsayarmu ta taimakawa Gaza ba,sannan kuma ya kara da cewa; Abinda Isra’ila makiya ke son yi, shi ne a kyale ta yi yadda take so da Falasdinawa ba tare da an mayar mata da martani ba daga kowace kasa ta musulmi.
Shugaban kungiyar ta Ansarullah ya kuma ce; Matsayar da kasar Yemen take dauka na taimakawa Falasdinawa, matsaya ce ta addini.”
Haka nan kuma ya kara da cewa; Daga cikin manufofin harin na Isra’ila a filin saukar jiragen sama na Sanaa da akwai dakatar da jigilar mahajjata, amma ba za su yi nasara ba.”
Shugaban kungiyar ta Ansarullah ya yi ishara da wahalhalun da al’ummar Gaza suke ciki,sannan kuma ya ce; A wannan lokacin wahalhalun na mutanen Falasdinu sun fi na baya, domin suna fuskantar yunwa da kuma ci gaba da kai hare-hare da Isra’ila take yi.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Makarantar ‘Ya’yan Sojoji Ta Zaria Ta Yi Bukin Cika Shekaru 70 Da Kafawa
Shugaban rundunar mayakan sama ta kasa,Air Marshal, Hassan Abubakar, ya bukaci tsoffin daliban makarantar ‘ya’yan sojoji dake Zaria watau NMS da su kasance masu kwazo da da’a a duk inda suke kamar yadda suka koya a makarantar.
Ya bayyana haka ne lokacin da ya ke jawabi a matsayin Babban bako na musamman a wurin bukin cika shekara 71 da aka gudanar a filin faretin RSM Zakari Kumasi dake harabar makarantar a zaria.
Shugaban rundunar mayakan saman ya bayyana cewa makarantar ta NMS ta yi fice wajen baiwa yara horo a fannonin karatu da kuma ilimin aikin soja wanda hakan ya sa ta samar da manyan sojoji da dama har ma da shi a ciki.
Air Marshal Abubakar ya ce bukin na da matukar muhimmanci gare shi,kasancewar sa tsohon dalibin makarantar.
A don haka sai ya yaba wa makarantar ta NMS bisa kasancewar ta akan turbar da aka santa da shi na samar da jajirtattun sojoji ga rundunar mayakan sama ta kasa tsawon shekaru 71 da kafa ta.
Shi ma a nashi jawabin, shugaban kungiyar tsoffin daliban makarantar, Laftana Kwamanda Sunday Ngegu mai ritaya, ya ce kasancewar shugaban rundunar mayakan sama tsohon dalibi a makarantar ya rinka taimaka wa kungiyar, inda ya bukaci sauran tsoffin daliban da suyi koyi da hakan.
Sunday Ngegu ya kuma yaba wa shugaban rundunar mayakan saman bisa gudunmuwar da ya baiwa kungiyar har ta samu nasarorin da ta samu.
Daliban makarantar sun gudanar da faretin ban girma ga manyan baki,yayin da kuma shugaban rundunar mayakan saman ya kaddamar da dakin shan magani na dalibin da babban dakin cin abinci tare da Kwamandan rundunar soji ta daya da sauran Kwamandodin rundunonin soja gami da mai masaukin baki na NMS.