A wani yunƙuri na ƙarfafa ilimi mai inganci, adalci da shigar da kowa a cikinsa ga yara da matasa a Jihar Kaduna, ƙungiyar Save the Children ta shirya taron bita na kwana biyu ga yan jarida da kungiyoyi masu zaman kansu a Kaduna.

 

Taron ya haɗa wakilai daga sashen ilimi, kafafen yaɗa labarai da ƙungiyoyin masu zaman kansu.

 

Taron wani ɓangare ne na babban shiri da ke da nufin haskaka ƙalubale da damar da ke akwai wajen dawo da yara makarantun da kuma tabbatar da samun ingantaccen ilimi.

 

Rahoton Hukumar Ƙididdiga ta Jihar Kaduna na shekarar 2020 ya nuna cewa fiye da yara dubu 700,000 ne basa zuwa makaranta a jihar – adadi mafi yawa a Najeriya.

 

Wannan matsala ta nuna bukatar daukar matakai na gaggawa da samarda domin kawar da duk wasu kalubale da ke hana yara shiga makaranta, ƙara adadin masu rajistar shiga makaranta da kuma inganta yadda ake koyarwa da koya.

 

Da yake jawabi a taron, Daraktan Tsare-tsare na Ma’aikatar Ilimi ta Jihar Kaduna, Malam Salisu Baba Lawal, tare da Mataimakin Shugaban Ayyuka, Hassan Abdul, sun tabbatar da cewa gwamnatin jihar na da niyyar rage adadin yaran da basa zuwa makaranta.

 

Sun bayyana cewa jihar na aiki tare da abokan haɗin gwiwa ciki har da Save the Children da UNICEF, domin shigar da yara akalla 200,000 cikin tsarin ilimi na yau da kullum.

 

Sun jaddada muhimmancin tabbatar da cewa shirin ya shafi kowane ɗalibi, musamman masu buƙatu na musamman.

 

Sun bayyana cewa aiwatar da wannan shiri mai da hankali kan yara yana da matuƙar muhimmanci, musamman a makarantun da ke da yawan yara masu cutar autism, domin hakan zai iya haɓaka ingancin karatu da tabbatar da cewa ba a bar ko wane yaro a baya ba.

 

Wadanda suka halarci taron sun jaddada rawar da kafafen yaɗa labarai ke takawa wajen wayar da kai da kuma ƙarfafa fafutukar neman ilimi mai shigar da kowa.

 

Daya daga cikin manyan abubuwan da aka cimma a taron shi ne tsara shirin tallata batun yara da basa zuwa makaranta ta hanyar amfani da labarun rayuwa, fasahar da muradun yara domin tasiri ga manufofi da kuma ƙarfafa haɗin kan al’umma.

 

Shugaban Ƙungiyar ‘Yan Jarida ta Najeriya (NUJ), reshen Jihar Kaduna, Malam AbdulGhaffar Alabewele, ya yaba wa masu shirya taron bisa yadda suka haɗa ‘yan jarida tun daga farko.

 

Ya ce hakan zai taimaka wajen fahimtar shirin da kyau da kuma samar da haɗin kai mai ma’ana.

 

Wani mahalarci daga Radio Nigeria Kaduna, Malam Adamu Yusuf, ya roƙi Gwamnatin Jihar Kaduna da ta ɗauki malamai ƙwararru a makarantun firamare, musamman a cikin yankunan karkara da ke da buƙata sosai.

 

Wasu daga cikin mahalarta sun bayyana taron a matsayin Wanda ya zo a lokacin da ya dace la’akari da yawan yara masu cutar autism da ke ƙaruwa da kuma buƙatar ƙarin tsarin tallafi.

 

Wani daga cikin mahalartan ya jaddada muhimmancin fara shirye-shiryen gwamnati da ke mai da hankali kan yara masu buƙatu na musamman, yana mai cewa fara tun da wuri yana da matuƙar tasiri wajen gina makoma mai haɗin kai da ci gaba.

 

A lokacin taron, an gabatar da bayanai daban-daban da suka bayyana manyan ƙalubalen da ilimi ke fuskanta a Jihar Kaduna da kuma hanyoyin aiwatar da shirin shekaru huɗu cikin nasara domin tabbatar da cewa kowane yaro ya samu ilimi mai nagarta.

 

Wannan shiri wani ɓangare ne na babban yunƙuri domin tabbatar da cewa dukkan yara a Jihar Kaduna—ko daga wane asali ko halin rayuwa—an ba su damar koyo, girma da cimma burinsu a rayuwa.

 

COV: Adamu Yusuf

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Yan Jarida Shirya Taron

এছাড়াও পড়ুন:

Kotu ta dakatar da babban taron PDP

Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta dakatar da jam’iyyar PDP daga gudanar babban taronta na ƙasa da aka shirya yi a Ibadan, Babban Birnin Jihar Oyo, a watan gobe.

Mai shari’a James Omotosho ne, ya bayar da wannan umarni, yayin da yake yanke hukunci kan wata ƙara da aka shigar domin sanin ko jam’iyyar PDP na da ikon ci gaba da shirya taron da aka tsara gudanarwa a ranakun 15 da 16 ga Nuwamba.

Real Madrid zata nemi diyyar Dala bilyan 4 daga UEFA An raba wa iyalan jami’an ’yan sandan da suka rasu a bakin aiki a Borno N63.4m

Waɗanda suka shigar da ƙarar sun haɗa da Austine Nwachukwu, shugaban PDP na Jihar Imo; Amah Abraham Nnanna, shugaban PDP na Jihar Abiya da Turnah George, sakataren PDP na yankin Kudu maso Kudu.

Waɗanda ake ƙarar sun haɗa da Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC), PDP, Sakataren Jam’iyyar na Ƙasa, Samuel Anyanwu, Sakataren shirya taruka na jam’iyyar, Umar Bature, Kwamitin Ayyuka na jam’iyyar na Ƙasa (NWC) da Kwamitin Zartarwa na jam’iyyar na Ƙasa (NEC).

Masu shigar da ƙarar sun kasance ’yan tsahin Nyesom Wike ne.

Sun roƙi kotu da ta hana gudanar da taron, inda suka bayyana cewar jam’iyyar ta saɓa wa dokokinta, Kundin Tsarin Mulkin Najeriya na 1999, da kuma Dokar Zaɓe wajen shirya taron.

Lauyansu ya shaida wa kotu cewa: “Ba a gudanar da taron wakilai a jihohi 14 ba don haka shirin taron ya saɓa wa doka.”

Sai dai PDP ta kare kanta, inda ta ce lamarin na harkokin cikin gidan jam’iyyar ne, don haka bai kamata kotu ta tsoma baki ba.

Jam’iyyar ta zargi masu ƙarar da ƙoƙarin tayar da rikici domin hana ta gudanar da sabon zaɓen shugabanni.

Aminiya ta ruwaito cewa wannan rikici ya ƙara dagula al’amura a jam’iyyar PDP.

Sakataren jam’iyyar na ƙasa, Sanata Samuel Anyanwu, a baya ya yi zargin cewa an yi amfani da hannunsa na bogi a takardun da aka aike wa INEC game da shirya taron.

Amma shugabancin jam’iyyar ya ƙaryata wannan zargi.

A halin yanzu, Kwamitin Shirya Taron na Ƙasa (NCOC) ya ɗage tantance ’yan takara da aka tsara gudanarwa a ranar 28 ga watan Oktoba.

Mutane da dama na ganin ɗage tantance ’yan takarae na da nasaba da jiran sakamakon hukuncin kotu kafin a ci gaba da shirye-shirye.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamna Uba Sani Ya Bayyana Tsare-tsaren Ci Gaban Kaduna a Taron Duniya a Dubai.
  • Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa
  • Kotu ta dakatar da gudanar da babban taron PDP
  • Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 
  • Gwamnatin Yobe ta ƙaddamar da shirin amfani da ma’adanai
  • Kotu ta dakatar da babban taron PDP
  • Shugabannin Kudancin Kaduna za su karrama Janar  Christopher Musa 
  • Ranar Foliyo Ta Duniya: Muna Fatan Ganin Karshen Cutar Foliyo A Jihar Katsina -Zulaihat Dikko Radda
  • NAJERIYA A YAU: Dalilan Da Daliban Makarantar Kudi Suka Fi Na Gwamnati Kokari
  • Ƙungiyar Rays Heaven ta Ƙarfafa Wayar da Kai kan Lafiyar Kwakwalwa a Kaduna