Save The Children Ta Shirya Taron Bita Ga Yan Jarida Da Kungiyoyi Masu Zaman Kansu A Kaduna.
Published: 31st, May 2025 GMT
A wani yunƙuri na ƙarfafa ilimi mai inganci, adalci da shigar da kowa a cikinsa ga yara da matasa a Jihar Kaduna, ƙungiyar Save the Children ta shirya taron bita na kwana biyu ga yan jarida da kungiyoyi masu zaman kansu a Kaduna.
Taron ya haɗa wakilai daga sashen ilimi, kafafen yaɗa labarai da ƙungiyoyin masu zaman kansu.
Taron wani ɓangare ne na babban shiri da ke da nufin haskaka ƙalubale da damar da ke akwai wajen dawo da yara makarantun da kuma tabbatar da samun ingantaccen ilimi.
Rahoton Hukumar Ƙididdiga ta Jihar Kaduna na shekarar 2020 ya nuna cewa fiye da yara dubu 700,000 ne basa zuwa makaranta a jihar – adadi mafi yawa a Najeriya.
Wannan matsala ta nuna bukatar daukar matakai na gaggawa da samarda domin kawar da duk wasu kalubale da ke hana yara shiga makaranta, ƙara adadin masu rajistar shiga makaranta da kuma inganta yadda ake koyarwa da koya.
Da yake jawabi a taron, Daraktan Tsare-tsare na Ma’aikatar Ilimi ta Jihar Kaduna, Malam Salisu Baba Lawal, tare da Mataimakin Shugaban Ayyuka, Hassan Abdul, sun tabbatar da cewa gwamnatin jihar na da niyyar rage adadin yaran da basa zuwa makaranta.
Sun bayyana cewa jihar na aiki tare da abokan haɗin gwiwa ciki har da Save the Children da UNICEF, domin shigar da yara akalla 200,000 cikin tsarin ilimi na yau da kullum.
Sun jaddada muhimmancin tabbatar da cewa shirin ya shafi kowane ɗalibi, musamman masu buƙatu na musamman.
Sun bayyana cewa aiwatar da wannan shiri mai da hankali kan yara yana da matuƙar muhimmanci, musamman a makarantun da ke da yawan yara masu cutar autism, domin hakan zai iya haɓaka ingancin karatu da tabbatar da cewa ba a bar ko wane yaro a baya ba.
Wadanda suka halarci taron sun jaddada rawar da kafafen yaɗa labarai ke takawa wajen wayar da kai da kuma ƙarfafa fafutukar neman ilimi mai shigar da kowa.
Daya daga cikin manyan abubuwan da aka cimma a taron shi ne tsara shirin tallata batun yara da basa zuwa makaranta ta hanyar amfani da labarun rayuwa, fasahar da muradun yara domin tasiri ga manufofi da kuma ƙarfafa haɗin kan al’umma.
Shugaban Ƙungiyar ‘Yan Jarida ta Najeriya (NUJ), reshen Jihar Kaduna, Malam AbdulGhaffar Alabewele, ya yaba wa masu shirya taron bisa yadda suka haɗa ‘yan jarida tun daga farko.
Ya ce hakan zai taimaka wajen fahimtar shirin da kyau da kuma samar da haɗin kai mai ma’ana.
Wani mahalarci daga Radio Nigeria Kaduna, Malam Adamu Yusuf, ya roƙi Gwamnatin Jihar Kaduna da ta ɗauki malamai ƙwararru a makarantun firamare, musamman a cikin yankunan karkara da ke da buƙata sosai.
Wasu daga cikin mahalarta sun bayyana taron a matsayin Wanda ya zo a lokacin da ya dace la’akari da yawan yara masu cutar autism da ke ƙaruwa da kuma buƙatar ƙarin tsarin tallafi.
Wani daga cikin mahalartan ya jaddada muhimmancin fara shirye-shiryen gwamnati da ke mai da hankali kan yara masu buƙatu na musamman, yana mai cewa fara tun da wuri yana da matuƙar tasiri wajen gina makoma mai haɗin kai da ci gaba.
A lokacin taron, an gabatar da bayanai daban-daban da suka bayyana manyan ƙalubalen da ilimi ke fuskanta a Jihar Kaduna da kuma hanyoyin aiwatar da shirin shekaru huɗu cikin nasara domin tabbatar da cewa kowane yaro ya samu ilimi mai nagarta.
Wannan shiri wani ɓangare ne na babban yunƙuri domin tabbatar da cewa dukkan yara a Jihar Kaduna—ko daga wane asali ko halin rayuwa—an ba su damar koyo, girma da cimma burinsu a rayuwa.
COV: Adamu Yusuf
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Yan Jarida Shirya Taron
এছাড়াও পড়ুন:
Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi
Wannan shi ne babban abin alfahari da Ministan Harkokin Waje, Ambasada Yusuf Maitama Tuggar ke jagoranta. A yayin tattaunawar manyan jami’an biyu a Berlin tare da ministan harkokin wajen Jamus Johann Wadephul, Tuggar ya nuna bajinta. “Ba manufar Nijeriya bace ta fitar da mutane zuwa wasu kasashen waje ba, sai don nuna gwanayenta,” in ji shi, tare da sake sanya haske a manufinta.
A cikin shekarun baya-bayan nan, yawan al’ummar Nijeriya sun kasance ana sanya su a matsayin wadanda ke cikin rikici, miliyoyin matasa marasa aikin yi, masu karatun digiri, da kwararru an nuna musu halin ko-in-kula.
Amma Tuggar, gogaggen jami’in diflomasiyya kuma mai tunani na Afirka, yana ganin abin da mutane da yawa ke watsi da shi dama ce. Ana ganin sama da mutum miliyan 220 da muke da su a yau ana hasashen za su kai miliyan 400 nan da shekarar 2050, don haka Nijeriya ba kawai mai daukar nauyin al’umma bace, ita ce ma’adanin jari-hujja baki daya.
Sabanin haka, Jamus da yawancin Tarayyar Turai suna tsufa da wuri. Tattalin arzikinsu na karuwa, amma yawansu yana raguwa
Kwararrun ma’aikata suna cikin karancin wadata. Vangaren kiwon lafiya ya tabarbare. Masana’antu suna bukatar a karfafe su da kwarewar dijital.
To a nan akwa al’amari mai ban sha’awa: Nijeriya na da hazaka. Turai kuma na da bukata. Amma maimakon a yi asarar wannan wannan hadin gwiwa ta hanyar yanke kauna da yin hijira ba bisa ka’ida ba, Tuggar ya ba da shawarar yin doka, da tsarin hadin gwiwa, wacce za a rika yin hijrar akan tsari.
Wadephul, a nasa bangaren, wannan shawara ba wai ta kasance karbabbiya bace, ai bayan haka abar sha’ace a bayyane
A nasa jawabin, ya jaddada ingancin zurfafa hadin gwiwa tsakanin Nijeriya da Jamus a fannonin da suka hada da kasuwanci zuwa makamashi, da kuma yadda ake tafiyar da ayyuka na hazaka. “Akwai manyan damammaki a hadin gwiwa cikin ma’adanai masu mahimmanci, canjin makamashi, da hadin gwiwar kamfanoni masu zaman kansu,” in ji shi.
Jamus ba ta sanya Nijeriya cikin masu ba da taimako ga masu karba, ko mai taimako ga marasa galihu. Madadin haka, wannan hadin gwiwa ne da zai zama na masu daidaita kasashen da za su daidata bukatun juna da mutunta juna. Tuggar da Wadephul sun binciko hanyoyin zurfafa alaka ta hanyar koyar da sana’o’i, inganta kwarewa, da kirkirar hanyoyin kaura da ke mutunta ikon mallaka da samun dama.
Hadin gwiwar makamashi tsakanin Jamus da Nijeriya, wanda aka fara a 2008 kuma aka karfafa shi a 2021 tare da kafa ofishin hydrogen a Abuja, wani abin koyi ne na yadda kasashen biyu za su iya samar da darajar kayan. Yanzu dai, makasudin yin haka shi ne a sake dawo da irin wannan hadin gwiwa, karfafawa matasa, da sanya hannun jari na kasashen biyu.
A cikin manufofin waje na Tuggar, ba gwaninta bace a rika fita da kaya ta hanyar bazata ba, domin kadara ta kasa. Ya fahimci cewa idan kaura ba ta da tsari, to lallai kasashe sun yi hasara. Amma idan aka yi da kyakkwar niyya kuma ana yin mubaya’a, al’ummomi kasashe za su shigo ciki.
’Yan Najeriya kwararrun da ke aiki a Berlin, Hamburg, Munich, ko Frankfurt ba wai kawai suna cike gibin aiki bane, suna gina gadoji na kasashen waje, aika kudi, samun sabbin kwarewa, da fadada darajar Nijeriya a duniya.
Wannan ba maganar hijira ba ce kawai; wannan shi ne dabarun diflomasiyya.
Wannan tsarin ya kalubalanci ra’ayin da aka dade ana yi wanda Afirka ba ta da wani abin da za ta iya bayarwa. Akasin haka, Afirka, da Nijeriya musamman a shirye suke domin kerawa gami da ba wa duniya abin da ba ta da shi ko take rasawa.
Ayyukan Tuggar a Berlin sun fi ba da fifiko kan kiraye-kirayen girmamawa na bangarorin biyu, da suka kasance wani bangare na hangen nesa wajen sake mayar da Nijeriya a matsayin mai kwarin gwiwa, mai kwarewa wajen taka muhimmiyar rawa a fagen duniya. Har ila yau ya gana da ‘yan majalisar dokokin Jamus, da manyan jami’an raya kasa, da Farfesa Lanz Rolla, wanda shi ne mai hangen nesan da ya kafa taron tattaunawa na duniya na Berlin.
Dangane da jagorancinsa da kuma yadda Nijeriya ke tasowa, an gayyaci Tuggar a hukumance don yin jawabi a taron 2025 na Tattaunawar Duniya ta Berlin. Wannan gayyata kakkarfar alama ce.
Kuma hakan ya tabbatar da rawar da Nijeriya ta taka wajen tsara tattaunawar duniya game da mulki, da dorewa, da kuma yin hijira.
Shekaru da yawa, an yi magana game da Afirka a cikin da’irar duniya. Tuggar yana son Nijeriya ta kasance daya daga cikin masu fada a ji kuma masu jagoranci.
Lokaci ya yi da ‘yan Nijeriya a gida da waje za su daina kallon hijira a matsayin abin takaici. Ba koyaushe ne hijrar take zama tsrewa ake ba,. Wani lokaci, ana ficewa ne domin fadada ilimi. Wani lokaci, masu hijrar ba batu ne na watsar da kasarsu ba, a’a suna fita ne domin ciyar da ita kasar gaba.
Dole ne mu gina tsarin da zai ba matasa ‘yan Nijeriya kayan aiki ba kawai don yin gasa a duniya ba sai don yin nasara da alfahari, daukar su tare da girmamawa, da kuma danganta nasarar kansu ga ci gaban kasa.
Dan Nijeriya mazaunin kasar waje ai ba zama dan kasa ba. Kadara ce kawai ta ketare.
Don yin wannan aikin, dole ne gwamnati ta saka hannun jari a fannin ilimi, fasahar dijital, da horar da sana’o’i. Dole ne kuma ta sake fasalin ayyukan diflomasiyya don tallafa wa hanyoyin kaura na doka da kuma kare ‘yan kasa a kasashen waje daga cin zarafi da nuna wariya.
Amma bayan gwamnati, dole ne kowane dan Najeriya ya sake gyara tunaninsa. “Japa” ba shi ne abin kunya ba. A hannun shugabanni masu hangen nesa kamar Tuggar, ya zama dabara dabara ta hawa abin hawa mai mahimmanci ga kasa.
Kada mu yi la’akari da bin hanya daya. Mu horar da ingantattun tunani, mu samar da ginshikai masu karfi, domin gina Nijeriya a duniya wanda zai amfanar da kowa.
Nijeriya ba ta yi asarar mutanenta ba. Tana amfanuwa ta karkashin kasa.
Kuma yayin da wannan sabon babi ya bayyana-mai tushe cikin mutunci, da tsarin diflomasiyya – har yanzu muna iya gano cewa jiragen da a da suka kwashe mafarkinmu suna dawowa, ba kawai tare da fasinjoji ba, har ma da kyakkyawar manufa.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp