Jagoran juyin juya halin Musulunci ya jaddada cewa: Dole ne a dauki kwararan matakai don dakatar da laifukan da ake yi a Gaza

A yayin ganawarsa da fira ministan Pakistan Shehbaz Sharif da tawagarsa a yammacin yau, Jagoran juyin juya halin Musulunci Ayatullah Sayyid Ali Khamenei ya jaddada wajabcin gudanar da ayyukan hadin gwiwa da inganci tsakanin kasashen Iran da Pakistan domin dakile laifukan da yahudawan sahayoniyya suke aikatawa a Gaza.

A farkon taron, Jagoran juyin juya halin Musulunci ya bayyana matsayin Pakistan na musamman a duniyar Musulunci, inda ya bayyana jin dadinsa da kawo karshen yakin da ake yi tsakanin Pakistan da Indiya, tare da bayyana fatansa na warware sabanin da ke tsakanin kasashen biyu ta hanyar lumana.

Haka nan kuma ya yi ishara da matsayar da Pakistan ta dauka kan batun Falastinu a cikin wadannan shekaru da suka gabata, yana mai cewa: Duk da cewa a cikin ‘yan shekarun nan a kodayaushe ana fuskantar kalubale ga kasashen musulmi na kulla alaka da yahudawan sahayoniyya, Pakistan ba ta taba samun irin wadannan fitintinu ba.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Hare-Haren HKI Kan Wata Makaranta A Gaza Ya Kashe Mutane 46 Daga Ciki Harda Yara Kanana

Wasu hare-haren da HKI ta kai kan gaza sun fada kan wata makaranta wacce aka maida ita wurin kwana, inda ya zuwa yanzu mutane 46 suka yi shahada a yayinda wasu 31 suka ji rauni. Daga cikin wadanda suka rasa rayukansu har da yara kanana.

Tashar talabijan ta Presstv ta bayyana cewa zana ganin yara suna gudu a cikin wuta suna kokaron kubutar da kansu. Labarin ya kara da cewa makarantar tana unguwar Daraj na birnin Gaza, mai suna Fahmi al-Jarjawi. Majiyar kungiyar kula da fararen hula a gazar ta bayyana cewa yahudawan kai hare haren a safiyar yau litinin a lokacinda suke barci.

Labarin ya kara da cewa a cikin wadanda yahudawan suka kashe a Gaza, akwai Mohammad Al-kasih shugaban bangaren yansandan bincike na arewacin Gaza da Matarsa da yayansa.

Wata majiyar Palasdinawa ta bayyana cewa kafin hari a kan makarantar yahudawan sun kai hare kan wani gida a unguwar Thawra da birnin Gaza.

Manufar yahudawan dai shi ne mamayar dukkan gaza da kuma korar Falasdinawa daga yankin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaban  Iran na ziyarar aiki a kasar Oman
  • Kasar Ireland Ta Yi Dokar Hana Shigar Da Kayan Da Aka Kera A ” Isra’ila” Cikinta
  • Sin Za Ta Kara Zurfafa Dunkule Rawar Yankunan Raya Tattalin Arziki Da Fasahohi A Fannin Janyo Jarin Waje
  • Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Ta Jaddada Cewa: Ba Zata Taba Amincewa Da Batun Dakatar Da Sarrafa Uranium Ba
  • Akwai Ma’ana Mai Zurfi A Bayan Da’a
  • Gwamnati Ta Kammala Samar Da Fasfo Sama Da 200,000 Da Suka Yi Jinkiri
  • Firaministan Pakistan na ziyara Tehran mai manufar inganta dangantaka tsakanin kasashen biyu
  • Babu Wasu Masu Juya Tinubu Ta Bayan Fage Ministan Yaɗa Labarai
  • Hare-Haren HKI Kan Wata Makaranta A Gaza Ya Kashe Mutane 46 Daga Ciki Harda Yara Kanana