Kungiyar kare hakkin bil’aama ta “Amnesty International” ta bayyana cewa; mai yiyuwa ne kungiyar ‘yan tawaye ta m23 da kuma sojojin gwamnatin DRC sun aikata laifukan yaki.

A wani rahoto da aka buga a jiya Talata, kungiyar kare hakkin bil’adam ta ce; Kungiyar M23 wacce take samun goyon bayan kasar Rwanda ta kashe mutane da dama, da kuma azabtar da su bayan da ta tsare su.

Kungiyar ta M23 ta kwace iko da yankin gabashin kasar mai cike da albarkatun karkashin kasa da su ka hada Bukavu da Goma.

Tare da cewa an kulla yarjejeniya a tsakanin M23 da gwamnatin DRC sai dai kuma har yanzu suna ci gaba da fada.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Ta Jaddada Cewa: Ba Zata Taba Amincewa Da Batun Dakatar Da Sarrafa Uranium Ba

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran ya jaddada cewa: Iran ba za ta daina sarrafa sinadarin Uranium a kowane hali ba

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran Isma’il Baqa’i ya tabbatar a wata hira da tashar CNN ta Amurka cewa: Iran ba za ta taba yin watsi da hakkinta na tace sinadarin Uranium a kowane hali ba.

A yayin da yake mayar da martani game da kyakkyawan fata na shugaban Amurka Donald Trump game da shawarwarin nukiliyar da aka yi tsakanin gwamnatinsa da Iran da kuma yadda yake kallon ci gaban da aka cimma, Baqa’i ya ce: Idan manufar Amurka ita ce tabbatar da cewa shirin makamashin nukiliyar Iran ba zata yi amfani da shi wajen karfin soji ba, to yana ganin za a iya cimma hakan cikin sauki. To amma idan har Amurka tana son tauye wa Iraniyawa ‘yancinsu na samun cikakken fasahar makamashin nukiliya na zaman lafiya da lumana ne, to yana ganin hakan zai zama babbar matsala, ta yadda Iran za ta kalubalanci dukkan tsarin.

A lokacin da wakilin tashar CNN ya tambaye shi: Shin ko suna tsammanin gwamnatin Trump da mai shiga tsakaninta, Witkoff, sun gane kuma sun fahimci hakan? Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran ya mayar da martani da cewa: Kasancewar Iran tana ci gaba da tattaunawa ya zuwa yanzu tana nufin cewa ta san akwai wani matakin fahimtar da Iran ba za ta iya ba a kowane irin yanayi ta yi watsi da haƙƙinta na mallakar fasahar makamashin nukiliya na zaman lafiya da lumana da suka haɗa da inganta sinadarin Uranium.

Amurka

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kasar Iran, Da Kasashen Kungiyar BRICS Sun Gudanar Da Taro Kan Harkokin Tsaro A Mosco
  • OPEC+ Ta Fara Shirin Ayyana Yawan Man Fetur Da Zata Haka Zuwa Sekara Ta 2027
  • Kungiyar ASEAN Ta Bayyana Damuwarta Da Kissan Kiyashi A gaza
  •  Yemen: Wuce Gona Da Irin HKI Ba Zai Sauya Mana Ra’ayi Akan Ci Gaba Da Taimaka Wa Gaza Ba
  • Red Crescent ta Iran da Red Cross ta Saliyo sun cimma yarjejeniyoyi da dama a tsakaninsu
  • Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Ta Jaddada Cewa: Ba Zata Taba Amincewa Da Batun Dakatar Da Sarrafa Uranium Ba
  • Ko Mene Ne Dalilin Da Ya Sa Trump Ya Gujewa Yaki Da Yemen Har Ya Kai Ga Fusata Kawayen Amurka
  • Hukumar Kare Hakkin Bil’adam Ta MDD Ta Bukaci A Kawo Karshen Kissan Kiyashi A Gaza
  • Gaza : Spain ta bukaci kasashen duniya su kakabawa Isra’ila takunkumi