Gwamnatin Yobe Ta Ɗauki Jami’an Kiwon Lafiya 42 Aiki
Published: 16th, February 2025 GMT
Hukumar kula da lafiya a matakin farko ta Jihar Yobe ta dauki ma’aikatan jinya 42 aiki domin inganta ayyukan kiwon lafiya a jihar.
Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da kakakin hukumar Adamu Abba ya fitar a Damaturu.
Kifi jinsin Shark ya fusata ya fasa rufin gida Mazabar Tsanyawa/Kunchi ta shafe shekara guda ba tare da wakilci baYa ce tuni babban sakataren hukumar Babagana Machina ya gabatar da wasikun nadin aiki ga ma’aikatan jinya da aka zabo wadanda suka kammala karatun horon su daga kwalejin jinya da ungozoma ta Shehu Sule da ke Damaturu.
Abba ya kara da cewa ma’aikatan jinya za su cike gibin ma’aikata a cibiyoyin kula da lafiya a matakin farko na kananan hukumomi 17 na jihar.
“Gwamnatin Mai Mala Buni ya zuwa yanzu, ta gyara tare da gina sabbin cibiyoyin kiwon lafiya na matakin farko guda 142 a fadin jihar tun daga shekarar 2019.
“Tun lokacin yakin neman zaben da karo na biyu gwamnan ya yi alkawarin samar da ingantaccen cibiyar kula da lafiya a matakin farko a mazabun 178 da ke Jihar Yobe.
“Saboda haka, wannan daukar ma’aikata da aka yi za su ƙara ƙarfin ma’aikata a cibiyoyin don inganta aikin na kiwon lafiya” in Jin Abba.
Sakataren hukumar, Babagana Machina ya taya ma’aikatan jinya murna yana mai umartar da su mayar da hankali wajen sadaukar da kansu ga ayyukansu.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Jihar Yobe jinya Kiwon Lafiya ma aikatan jinya a matakin farko
এছাড়াও পড়ুন:
Boko Haram ta kashe masu zaman makoki 7 a Chibok
Mayaƙan ƙungiyar Boko Haram sun kashe masu zaman makoki bakwai tare da jikkata wasu a ƙauyen Kopl da ke Ƙaramar Hukumar Chibok ta Jihar Borno.
Shugaban Karamar Hukumar, Honorabul Modu Mustapha, ya ce mayaƙan sun buɗe wa mutanen wuta ne a yammacin ranar Litinin, a yayin da suke shirin gudanar da addu’o’i ga ’yan uwansu da suka rasu.
Ya ce, “Sun taru ne domin yin addu’a lokacin da ’yan ta’addan suka sauka a kansu. Mun kwashe mutane da yawa da suka samu raunukan harsashi zuwa Babban Asibitin Mubi da ke maƙwabtaka da Jihar Adamawa.
“Adadin waɗanda suka mutu na iya ƙaruwa, saboda wasu sun tsere cikin daji da raunukan harsashi. Ana ci gaba da aikin nemowa da ceto waɗanda ke cikin daji,” in ji shi.
Bom ɗin Boko Haram ya kashe mutane 26 a Borno NAJERIYA A YAU: Dalilin karyewar farashin shinkafa a kasuwannin Najeriya Shugaban Majalisar Ƙoli ta Shari’ar Musulunci a Najeriya ya rasuSanatan Borno ta Kudu, Ali Ndume, ya ci gaba da yin Allah wadai da hare-haren, inda ya bayyana halin da ake ciki a matsayin abin da ya wuce tunanin dan Adam.
“Ko jiya ma, na samu kiran gaggawa cewa an kashe sama da ’yan banga 10 a wani yankin da ke tsakanin Karamar Hukumar Hawul ta Jihar Borno da garin Garkida a Jihar Adamawa.
“Al’ummata na fama da munanan asara ba tare da wani faɗa ba. A cikin wata guda da ya gabata kaɗai, an kashe sama da mutum dari a hare-hare da dama yankunan Sabon Gari da Izge da Kirawa da Pulka da Damboada Chibok da Askira Uba da wasu da yawa da ba zan iya lissafawa ba,” in ji Sanata Ndume.