Shugaban rundunar mayakan sama ta kasa,Air Marshal, Hassan Abubakar, ya bukaci tsoffin daliban makarantar ‘ya’yan sojoji dake Zaria watau NMS da su kasance masu kwazo da da’a a duk inda suke kamar yadda suka koya a makarantar.

Ya bayyana haka ne lokacin da ya ke jawabi a matsayin Babban bako na musamman a wurin bukin cika shekara 71 da aka gudanar a filin faretin RSM Zakari Kumasi dake harabar makarantar a zaria.

Shugaban rundunar mayakan saman ya bayyana cewa makarantar ta NMS ta yi fice wajen baiwa yara horo a fannonin karatu da kuma ilimin aikin soja wanda hakan ya sa ta samar da manyan sojoji da dama har ma da shi a ciki.

Air Marshal Abubakar ya ce bukin na da matukar muhimmanci gare shi,kasancewar sa tsohon dalibin makarantar.

A don haka sai ya yaba wa makarantar ta NMS bisa kasancewar ta akan turbar da aka santa da shi na samar da jajirtattun sojoji ga rundunar mayakan sama ta kasa tsawon shekaru 71 da kafa ta.

Shi ma a nashi jawabin, shugaban kungiyar tsoffin daliban makarantar, Laftana Kwamanda Sunday Ngegu mai ritaya, ya ce kasancewar shugaban rundunar mayakan sama tsohon dalibi a makarantar ya rinka taimaka wa kungiyar, inda ya bukaci sauran tsoffin daliban da suyi koyi da hakan.

Sunday Ngegu ya kuma yaba wa shugaban rundunar mayakan saman bisa gudunmuwar da ya baiwa kungiyar har ta samu nasarorin da ta samu.

Daliban makarantar sun gudanar da faretin ban girma ga manyan baki,yayin da kuma shugaban rundunar mayakan saman ya kaddamar da dakin shan magani na dalibin da babban dakin cin abinci tare da Kwamandan rundunar soji ta daya da sauran Kwamandodin rundunonin soja gami da mai masaukin baki na NMS.

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Zaria shugaban rundunar mayakan a makarantar

এছাড়াও পড়ুন:

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Da Dama A Wani Sabon Hari Da Suka Kai Sansanin Sojoji A Borno

A cewar Mukaddashin Daraktan, ‘yan ta’addar sun yi yunkurin kutsawa inda sojojin suke, amma suka gamu da karfin soji.

 

Ya kara da cewa, Rundunar Sojan Sama ta bayar da bayanan sirri tare da karfafawa sojin kasa, wanda ya kai ga halaka sauran ‘yan ta’addan da suka tsere.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ɗalibai sun maƙale lokacin da gini ya rufta suna jarrabawa
  •  Yemen: Wuce Gona Da Irin HKI Ba Zai Sauya Mana Ra’ayi Akan Ci Gaba Da Taimaka Wa Gaza Ba
  • Babu Wata Sauran Mafaka Ga ‘Yan Ta’adda, In Ji Shugaban Rundunar Sojin Sama
  • An Kama Sojoji 18 Da ‘Yansanda 15 Da Suke Siyar Da Makamai Ga ‘Yan Ta’adda
  • Sojoji sun halaka mayakan ISWAP da dama a Borno
  • Sojoji Sun Koka Bisa Jinkirin Yanke wa Ƴan Ta’adda 1,450 Hukunci
  • Wata Hajiya ‘Yar Nijeriya Mai Shekaru 75 Ta Rasu A Saudiyya Yayin Aikin Hajji
  • Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Da Dama A Wani Sabon Hari Da Suka Kai Sansanin Sojoji A Borno
  • Hukumar Kare Hakkin Bil’adam Ta MDD Ta Bukaci A Kawo Karshen Kissan Kiyashi A Gaza