Mene ne dalilin da ya sa Amurka da Isra’ila suke barazanar jefa bama-baman nukiliya a Gaza?

Masanin siyasa kuma mai sharhi Abdel Bari Atwan ya rubuta labarin game da barazanar da Amurka ta yi na kai wa Gaza hari da makamin nukiliya, yana mai cewa; “Domin dan majalisar wakilai na jam’iyyar Republican Randy Fein ya yi kira da a kai hari kan Zirin Gaza da bama-baman nukiliya, kwatankwacin abin da kasarsa ta yi a Hiroshima da Nagasaki na Japan, a karshen yakin duniya na biyu, da kuma samun wanda ya yaba masa a gwamnatin Shugaba Donald Trump, wannan shi ne kololuwar ta’addanci, rashin mutuntaka, da kishir ruwan zubar da jini a duniya daga jagororin da ke da’awar kare hakkin bil’adama a duniya kuma daga kasar da ta fi kowace kasa da’awar kare hakkin bil’adama da neman wanzar da adalci a fadin duniya.

Wani abin mamaki shi ne, wannan kira ya fito ne daga wani dan majalisar wakilai na jam’iyyar Republican wanda shugaba Trump ke goyon bayan yakin neman zabensa, da kuma abin takaici, har ma da wasu Larabawa masu kada kuri’a. Wannan kiran na kai harin makamashin Nukiliya ya zo ne a daidai lokacin da Trump ya dawo daga rangadin da ya kai wasu kasashen Larabawa uku, inda ya yi nasarar karbar dala tiriliyan 5, ciki har da wani jirgin sama na shugaban kasa a matsayin kyauta, wanda ya kai kusan rabin dala biliyan daya bayan da aka cika masa kayan aiki.

Wannan dan majalisar mai dauke da akidar ‘yan sahayoniyya ta nuna wariyar al’umma, da bai san adadin mutanen da Benjamin Netanyahu ya zubar da jininsu a yakin kisan kiyashin da ya jagoranta kan Gaza ba, wanda abin koyi ne a cikin kungiyar ‘yan Nazin zamani kuma wadanda ya kashe ya ninka adadin wadanda harin bam din nukiliya guda biyu da aka jefa kan biranen kasar Japan biyu. Kwatanta wannan da yawan al’ummar Zirin Gaza, wadanda ba su wuce miliyan biyu ba, da kuma al’ummar Japan, wadanda aka kiyasta kusan miliyan 124.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Jam’iyyar APC A Najeriya Ta Tabbatar Da Tinubu A Matsayin Dan Takarar Shugaban Kasa A Jam’iyyar A Shekara Ta 2027

Jam’iyyar ‘All Progressives Congress” (APC) mai Mulki a tarayyar Najeriya ta tabbatar da shugaban Bola Ahmed Tinubu a matsayin dan takarar Jam’iyyar a zaben shugaban kas ana shekara ta 2027 mai zuwa.

Shafin yada labarai na Afrika ya bayyana cewa a jiya Alhamis ce a taron Jam’iyyar wanda aka gudanar a Abuja, kuma wanda ya zo dai-dai da cika shekaru biyu da zagayensa na farko na shugabancin kasar Jam’iyyar ta nada shi Shugaba Bola Ahmed Tinubu dan shekara 73 a duniya a matsayin dan takararta a zaben na shekara ta 2027, don ya sami damar kamala shirinsa nag yare-gywaren tattalin arzikin kasar da y afara.

Shugaban Tinubu dai ya kara farashin man fetur a ranar da ya hau kan kujerar shugabancin kasar, ya kuma cire tallafin da gwamnati take yiwa farashin man, sannan ya kara haraji wanda duk sun hadu sun Sanya rayuwar mafi yawan mutanen kasar cikin bala’I wanda basu taba ganin irinsa .

Shirin nasa ya dadadawa manya-manyan cibiyoyin kudade a duniya wadanda ba ruwansu da rayuwar talaka a ko ina suke a duniya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ‘Yar Majalisar Dokokin Ireland Ta Yi Suka Kan Shugabannin Turai Tare Da Neman Afuwa Daga Falasdinawa
  • Hamas ta yi tir da kiran da dan majalisar dokokin Amurka ya yi na kai farmakin nukiliya a Gaza
  • Jonh Kerry Ya Ce HKI Ba Zata Iya Wargaza Cibiyoyin Nukliyar Kasar Iran ba
  •  Ana Mayar Da Martani Akan Dan Majalisar Amurka  Da Ya Yi Kira A Jefa Bom Din Nukiliya A Gaza
  • Sin Da ASEAN Sun Kammala Tattaunawa Game Da Kafa Yankin Ciniki Cikin ‘Yanci
  • ‘Yan Adawa Na Cacakar APC A Yankin Arewa Maso Yamma Bisa Goyon Bayan Tazarcen Tinubu
  • Wani Dan Majalisar Dokokin Kasar Amurka Ya Bukaci Amurka Ta Jefa Makaman Nukliya Kan Gaza
  • Jam’iyyar APC A Najeriya Ta Tabbatar Da Tinubu A Matsayin Dan Takarar Shugaban Kasa A Jam’iyyar A Shekara Ta 2027
  • Abin da muka sani kan labarin juyin mulki a Kwadebuwa