Mene Ne Dalilin Amurka Na Cewa Zata Harba Makamamin Nukiliya Kan Yankin Zirin Gaza?
Published: 25th, May 2025 GMT
Mene ne dalilin da ya sa Amurka da Isra’ila suke barazanar jefa bama-baman nukiliya a Gaza?
Masanin siyasa kuma mai sharhi Abdel Bari Atwan ya rubuta labarin game da barazanar da Amurka ta yi na kai wa Gaza hari da makamin nukiliya, yana mai cewa; “Domin dan majalisar wakilai na jam’iyyar Republican Randy Fein ya yi kira da a kai hari kan Zirin Gaza da bama-baman nukiliya, kwatankwacin abin da kasarsa ta yi a Hiroshima da Nagasaki na Japan, a karshen yakin duniya na biyu, da kuma samun wanda ya yaba masa a gwamnatin Shugaba Donald Trump, wannan shi ne kololuwar ta’addanci, rashin mutuntaka, da kishir ruwan zubar da jini a duniya daga jagororin da ke da’awar kare hakkin bil’adama a duniya kuma daga kasar da ta fi kowace kasa da’awar kare hakkin bil’adama da neman wanzar da adalci a fadin duniya.
Wani abin mamaki shi ne, wannan kira ya fito ne daga wani dan majalisar wakilai na jam’iyyar Republican wanda shugaba Trump ke goyon bayan yakin neman zabensa, da kuma abin takaici, har ma da wasu Larabawa masu kada kuri’a. Wannan kiran na kai harin makamashin Nukiliya ya zo ne a daidai lokacin da Trump ya dawo daga rangadin da ya kai wasu kasashen Larabawa uku, inda ya yi nasarar karbar dala tiriliyan 5, ciki har da wani jirgin sama na shugaban kasa a matsayin kyauta, wanda ya kai kusan rabin dala biliyan daya bayan da aka cika masa kayan aiki.
Wannan dan majalisar mai dauke da akidar ‘yan sahayoniyya ta nuna wariyar al’umma, da bai san adadin mutanen da Benjamin Netanyahu ya zubar da jininsu a yakin kisan kiyashin da ya jagoranta kan Gaza ba, wanda abin koyi ne a cikin kungiyar ‘yan Nazin zamani kuma wadanda ya kashe ya ninka adadin wadanda harin bam din nukiliya guda biyu da aka jefa kan biranen kasar Japan biyu. Kwatanta wannan da yawan al’ummar Zirin Gaza, wadanda ba su wuce miliyan biyu ba, da kuma al’ummar Japan, wadanda aka kiyasta kusan miliyan 124.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Real Madrid zata nemi diyyar Dala bilyan 4 daga UEFA
Wata kotu da ke birnin Madrid ta yi watsi da ƙarar da Hukumar ƙwallon ƙafa ta Nahiyyar Turai UEFA, LaLiga da Hukumar Kwallon Kafa ta Sipaniya suka shigar kan ƙin amincewa da gasar Super League.
Wannan yana nufin yanzu Real Madrid da sauran ƙungiyyoyin za su iya neman diyyar kudi Euro Milyan 4.
Kotu ta tsige dan majalisar da ya sauya sheka zuwa APC Shugabannin Kudancin Kaduna za su karrama Janar Christopher MusaReal Madrid ta ce, wannan hukuncin ya tabbatar da cewa UEFA ta karya dokokin gasa, kuma ƙungiyyoyi sun rasa maƙuden kuɗaɗe tun daga lokacin da aka dakatar da gasar.
Gasar wacce aka shirya farawa a shekarar 2021 tare da manyan ƙungiyoyin Turai, an yi hasashen zata samar da kusan Yuro miliyan 200 ga ƙungiyoyin da suka shiga.
A nata martanin hukumar UEFA ta dage cewa wannan sabon hukuncin ba ya nufin an dawo ko an amince da a buga gasar Super League ba ne.