Aminiya:
2025-07-23@22:47:36 GMT

Mutanen da suka rasu a ambaliyar ruwa a Neja sun ƙaru zuwa 151

Published: 31st, May 2025 GMT

Adadin mutanen da suka mutu a mummunar ibtila’in ambaliya a Jihar Neja ya karu zuwa mutum 151.

Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Jihar Neja (NSEMA) ce ta sanar cewa mutane 11 sun jikkata, yayin da mutane 3,018 suka rasa matsuguninsu a ibtila’in na ƙaramar hukumar Mokwa a safiyar Asabar.

Kakakin hukumar, Ibrahim Hussaini, ya bayyana cewa ambaliyar ta shafi gidaje 265 da kuma magidanta 503.

Ya ƙara da cewa yankuna uku, da suka hada da Tiffin Maza da Anguwan Hausawa, sun nutse sakamakon ruwan sama mai ƙarfi da aka yi na tsawon sa’o’i da dare a ranar Laraba.

Maƙabarta mai shekaru 500 da ta koma maɓoyar ’yan daba Sojoji sun kashe ɗan ta’adda da aka sa ladar N100m a kansa a Borno

Wannan lamari ya faru ne watanni biyar bayan Gwamnan Jihar Neja, Umar Bago, ya sanar da cewa jihar ta samu tallafin dala miliyan 10 daga Bankin Duniya don dakile zaizayar ƙasa a wasu sassan Mokwa.

Gwamnan ya ce an tantance kwararrun ’yan kwangila don gudanar da aikin.

A ranar Juma’a, Shugaban Ƙasa Bola Tinubu a yayin miƙa ta’aziyyarsa, ya umarci Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA) da hukumomin tsaro su ƙara ƙaimi wajen aikin ceto da agaji a wuraren da abin ya shafa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ambaliya Mokwa

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamna Sule Ya Ƙara Musanta Zargin Kare Ƴan Ta’adda A Nasarawa

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Cutar Amai Da Gudawa Ta Hallaka Mutane 13 A Neja
  • Sin Ta Yi Mu’amala Da Kasashen Dake Kan Karshen Kogin Yarlung Zangbo Dangane Da Batun Gina Tashar Samar Da Wutar Lantarki Ta Karfin Ruwa A Kogin
  • Matasa 3 sun rasu yayin wanka a rafi a Bauchi
  • Aikin Zirga-Zirgar Jiragen Sama Ta Fasinja Ta Sin Ya Bunkasa Zuwa Sabon Matsayi
  • Gwamna Sule Ya Ƙara Musanta Zargin Kare Ƴan Ta’adda A Nasarawa
  • NEDC ta raba wa mutanen da ambaliya ta shafa kayan gini a Yobe
  • Sin Ta Samar Da Karin Guraben Aikin Yi Miliyan 6.95 A Rabin Farko Na Bana
  • Magudnar Ruwa Ta Yi Ajalin Rayuka Hudu A Zangon Kaya, Kano
  • Mataimakiyar Shugaban Majalisar Dinkin Duniya Ta Jinjinawa Gwamnan Kano Bisa Ayyukan Cigaban Jihar
  • Jaridar Washington Post Ta Ce; Yeman Ta Gurguta Ayyukan Tashoshin Jiragen Ruwan Isra’ila