‘Yan Tawayen Sudan Sun Kashe Fararen Hula 10 A Hare-Haren Da Suka Kai Kan Birnin Kordofan
Published: 29th, May 2025 GMT
Fararen hula 10 ne suka rasa rayukansu sakamakon harin da jiragen yaki mara matuki suka kai kan birnin Kordofan na kasar Sudan
Kafofin yada labarai na cikin gidan kasar Sudan sun rawaito cewa: Akalla fararen hula 10 ne suka rasa rayukansu, wasu kuma suka jikkata sakamakon hare-haren da dakarun kai daukin gaggawa na Rapid Support Forces suka kai kan jihohin Yamma da Kudancin Kordofan.
Shafin yanar gizo na Sudan Tribune ya watsa rahoto cewa: Dakarun kai daukin gaggawa na Rapid Support Forces sun zafafa kai hare-hare ta sama a garuruwa da biranen yankin Kordofan tun farkon wannan wata.
Yankin dai ya sha fama da tashe tashen hankula tsakanin bangarorin da ke gaba da juna, inda kungiyar Rapid Support Forces ke da nufin dakile yunkurin sojojin Sudan da ke samun ci gaba a garuruwa da dama na Arewa, Yamma, da Kudancin Kordofan.
Shafin yanar gizo ya nakalto majiyar kasar na cewa: Akalla mutane 8 ne suka rasa rayukansu kana wasu 12 suka jikkata bayan da wani jirgin sama mara matuki na kungiyar Rapid Support Forces ya kai hari a kasuwar garin Al-Khawi da ke yammacin jihar Kordofan. Hakazalika an kai wani hari makamancin haka a wata unguwa da ke birnin Al-Dabaibat a jihar Kordofan ta Kudu, inda ya kashe fararen hula biyu tare da jikkata wasu biyar na daban. Haka nan jiragen yakin sun kai hari a wani sansanin soji a wannan birni, inda suka kashe sojoji tare da lalata motocin yaki.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: Rapid Support Forces
এছাড়াও পড়ুন:
Sojoji sun kashe Kwamandan Boko Haram Ibn Khalid a Borno
Dakarun Sojin Operation Hadin Kai, sun daƙile hare-haren Boko Haram a garuruwan Monguno da Bitta da ke Jihar Borno, tare da wani kashe babban Kwamandan Boko Haram mai suna Ibn Khalid.
Sun kuma kashe ’yan ta’adda da dama, ciki har da wani babban kwamandan ƙungiyar.
NAJERIYA A YAU: Cututtukan da rumar daki ke haifarwa ga jikin mutum Tinubu ya sake miƙa buƙatar karɓo bashin Dala miliyan 347 daga ƙetareMataimakin Daraktan Hulɗa da Jama’a na Rundunar, Kapten Reuben Kovangiya, ya ce sojojin sun yi jarumta wajen hana ’yan ta’addan shiga Monguno.
Ya ce sojojin sun yi amfani da manyan makamai wajen mayar da martani, inda suka kashe ‘yan ta’adda da dama, ciki har da wani babban kwamandan Boko Haram mai suna Ibn Khalid.
Yayin da sojojin ke bin sahun ’yan ta’addan da suka tsere, sun ga jini a hanya, alamar cewa wasu daga cikinsu sun jikkata.
Sojojin sun kuma ƙwato makamai da dama daga hannun ’yan ta’addan, ciki har da harsasai, PKT, ma’ajin bindiga AK-47, bam ɗin roka (RPG) da wasu kayayyaki.
Haka kuma, sun samu na’urar ɗaukar bidiyo da ’yan ta’addan ke amfani da ita.
A wasu hare-haren daban da suka gudana a wannan lokaci, sojojin sun kashe ƙarin mayaƙan Boko Haram 17 a dazukan Sambisa, Madagali da Kaga.
Haka kuma sun ƙwato babura da wasu kayan amfani daga hannunsu.
Shugabannin dakarun sun yaba da jarumtar sojojin, kuma sun buƙace su da su ci gaba da yaƙar ’yan ta’addan.