‘Yan Tawayen Sudan Sun Kashe Fararen Hula 10 A Hare-Haren Da Suka Kai Kan Birnin Kordofan
Published: 29th, May 2025 GMT
Fararen hula 10 ne suka rasa rayukansu sakamakon harin da jiragen yaki mara matuki suka kai kan birnin Kordofan na kasar Sudan
Kafofin yada labarai na cikin gidan kasar Sudan sun rawaito cewa: Akalla fararen hula 10 ne suka rasa rayukansu, wasu kuma suka jikkata sakamakon hare-haren da dakarun kai daukin gaggawa na Rapid Support Forces suka kai kan jihohin Yamma da Kudancin Kordofan.
Shafin yanar gizo na Sudan Tribune ya watsa rahoto cewa: Dakarun kai daukin gaggawa na Rapid Support Forces sun zafafa kai hare-hare ta sama a garuruwa da biranen yankin Kordofan tun farkon wannan wata.
Yankin dai ya sha fama da tashe tashen hankula tsakanin bangarorin da ke gaba da juna, inda kungiyar Rapid Support Forces ke da nufin dakile yunkurin sojojin Sudan da ke samun ci gaba a garuruwa da dama na Arewa, Yamma, da Kudancin Kordofan.
Shafin yanar gizo ya nakalto majiyar kasar na cewa: Akalla mutane 8 ne suka rasa rayukansu kana wasu 12 suka jikkata bayan da wani jirgin sama mara matuki na kungiyar Rapid Support Forces ya kai hari a kasuwar garin Al-Khawi da ke yammacin jihar Kordofan. Hakazalika an kai wani hari makamancin haka a wata unguwa da ke birnin Al-Dabaibat a jihar Kordofan ta Kudu, inda ya kashe fararen hula biyu tare da jikkata wasu biyar na daban. Haka nan jiragen yakin sun kai hari a wani sansanin soji a wannan birni, inda suka kashe sojoji tare da lalata motocin yaki.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: Rapid Support Forces
এছাড়াও পড়ুন:
’Yan bindiga sun kashe makiyaya 2, sun sace shanu 320 a Kaduna
Wasu ’yan bindiga sun kashe wasu makiyaya biyu da suka haɗa da: Mudda Shannon da Suleiman Bello, yayin da suka raunata ɗaya a ƙauyen Kurmin Lemu da ke ƙaramar hukumar Kagarko ta Jihar Kaduna.
Wani ɗan unguwar Kurim Lemu mai suna Shuaibu Ibrahim ya ce, lamarin ya faru ne a ranar Alhamis da misalin ƙarfe 12:07 na tsakar dare.
Ɗalibai sun maƙale lokacin da gini ya rufta suna jarrabawa Ko kwabo ban ciyo bashi ba tun da na zama Gwamnan Kaduna – Uba SaniYa ce, ’yan bindigar da suka zo adadi mai yawa tare miyagun makamai sun mamaye sansanin makiyayan inda suka buɗe wuta, inda suka kashe biyu daga cikin makiyayan nan take.
Ya ce, ɗaya daga cikin makiyayan ya tsallake rijiya da baya, amma ya samu raunukan harbin bindiga, inda ya ce ’yan bindigar sun je kai tsaye inda shanun ke da sansani suka kwashe su zuwa cikin dajin.
Ibrahim, ya ce daga baya an kai makiyayin da suka jikkata zuwa asibiti a garin Kagarko, inda yake jinya, kamar yadda ya ce an sanar da sojojin da ke Kagarko.
“An sanar da wasu sojojin da ke Kagarko, tun kafin su isa sansanin ’yan fashin sun tsere da shanun,” in ji shi.
Wani shugaban unguwar yankin da ya nemi a sakaya sunansa, shi ma ya tabbatar wa wakilinmu afkuwar lamarin ta wayar tarho.
Ya ce, ya samu rahoto daga ɗaya daga cikin shugabannin makiyaya na unguwar cewa ’yan bindiga sun kai hari sansanin makiyaya tare da kashe mutum biyu.
“Da safiyar yau ma na samu rahoto daga wani basaraken Fulani daga ƙauyen Kurmin Lemu cewa, wasu ’yan bindiga sun kai hari sansanin makiyaya inda suka kashe wasu Fulani biyu sannan suka yi awon gaba da shanunsu.” In ji shi.
Shugaban Unguwar ya bayyana cewa, ya kuma sanar da sojojin game da harin, duk da cewa ya ce an binne gawarwakin makiyayan biyu da suka mutu.
Kakakin rundunar ’yan sandan Jihar Kaduna, ASP Hassan Mansur ya zuwa yanzu bai tabbatar da faruwar lamarin ba, domin har zuwa lokacin da ake haɗa rahoton bai amsa kiran da aka yi masa ba.