Aminiya:
2025-06-01@20:33:18 GMT

Sojoji sun cafke ɗan ta’adda sun ƙwato makamai a Filato

Published: 31st, May 2025 GMT

Sojoji sun yi nasarar cafke wani mutum da ake zargi dan ta’adda ne tare da gano ma’adanar makamai a yayin wani samame da suka yi a Ƙaramar Hukumar Bassa ta Jihar Filato.

Binciken farko ya nuna cewa wanda aka kama ɗin yana da alaƙa da wata ƙungiyar masu aikata laifuka da ke da alhakin kisan wani makiyayi da satar shanu 1,250 a ƙauyen Tomborong, Ƙaramar Hukumar Riyom, a ranar 27 ga watan nan na Mayu.

A safiyar ranar Juma’a, sojoji suka kama wanda ake zargin, bayan samun rahoto game da inda ake zargin ɗan bangar yake ɓoye a ƙauyen Hura.

Yayin wani bincike da aka yi a maboyar wanda ake zargin, jami’an tsaro sun gano bindigar AK-47 guda daya, tare da harsasai 26 na 5.56mm da kuɗi da wasu abubuwan da ake zargin asiri ne.

Wata majiyar soji ta bayyana cewa wanda ake zargin yana tsare a hannun jami’an tsaro kuma yana “bayar da haɗin kai ga masu bincike kan sunaye da wuraren da sauran mambobin ƙungiyar da ma’adanar makamansu suke.”

Sojoji sun tsananta ƙoƙarin gano tare da kama sauran membobin ƙungiyar da ake zargi da alhakin ayyukan laifuka a yankin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ɗan Ta adda da ake zargin

এছাড়াও পড়ুন:

Kungiyar Hamas Ta Bukaci Masu Shiga Tsakani Amurkawa Su Gamsar da Ita Za’a Dakatar Da Yaki A Gaza

Kungiyar Hamas wacce take iko da zirin gaza ta bukaci masu shiga tsakanin Amurkawa su ngamtar da ita kan cewa HKI zata dakatar da yaki ta kuma fice daga zirin gaza. Amma shawarar da Steve Witkoff ya gabatar bata kunshi wani abu wanda zaia gamsar da kungiyar ta amince da wani sulhu ba.

Jihad Taha kakakin kungiyar ya bayyana cewa Hamas tana nazarin shawarar da Witskoff ya gabatar da tsagaita wuta a gaza wanda ya amince da dakatar da wuta na wucin gadi sannan a sake komawa yaki da kuma shigo a kayakin agaji. Y ace shawarar bata ambaci ficewar sojojin HKI daga yankin ba.

Taha ya bayyana cewa shawarar bata da wani abin dogaro wanda Hamas da kungiyoyin masu gwagwarmaya zasu riki na tsagaita wuta a gaza. Amma dukm da haka suna nazarinsa kuma zasu bayyana ra’yinsu nan gaba.

Ya Zuwa yanzu dai sojojin yahudawan sun kashe Falasdinawa fiye da 54000 a cikin shekara da rabi da suke fafatawa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Najeriya: An Bude Bincike Sojojin Da Suke Bayar Da Makamai Ga Kungiyoyi Masu Dauke Da Makamai
  • NDLEA Ta Cafke Masu Tura Alhazai Saudiyya Domin Safarar Hodar Iblis Zuwa Kasar
  • Iran Ta Kaddamarda Sabbin Magunguna Har 23 Tare Riga Kafin HPV A Karon Farko A Kasar
  • Indiya ta amsa cewa Pakistan ta kakkaɓo jiragen yaƙinta
  • Kungiyar Hamas Ta Bukaci Masu Shiga Tsakani Amurkawa Su Gamsar da Ita Za’a Dakatar Da Yaki A Gaza
  • Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (3)
  • Sojoji sun kashe ɗan ta’adda da aka sa ladar N100m a kansa a Bor
  • Sojoji Sun Kashe Ƴan Ta’adda 60 A Borno
  • An Kama Mutane 49 Da Ake Zargi Da Damfara A Jihar Kogi