Aminiya:
2025-07-24@23:19:48 GMT

Sojoji sun cafke ɗan ta’adda sun ƙwato makamai a Filato

Published: 31st, May 2025 GMT

Sojoji sun yi nasarar cafke wani mutum da ake zargi dan ta’adda ne tare da gano ma’adanar makamai a yayin wani samame da suka yi a Ƙaramar Hukumar Bassa ta Jihar Filato.

Binciken farko ya nuna cewa wanda aka kama ɗin yana da alaƙa da wata ƙungiyar masu aikata laifuka da ke da alhakin kisan wani makiyayi da satar shanu 1,250 a ƙauyen Tomborong, Ƙaramar Hukumar Riyom, a ranar 27 ga watan nan na Mayu.

A safiyar ranar Juma’a, sojoji suka kama wanda ake zargin, bayan samun rahoto game da inda ake zargin ɗan bangar yake ɓoye a ƙauyen Hura.

Yayin wani bincike da aka yi a maboyar wanda ake zargin, jami’an tsaro sun gano bindigar AK-47 guda daya, tare da harsasai 26 na 5.56mm da kuɗi da wasu abubuwan da ake zargin asiri ne.

Wata majiyar soji ta bayyana cewa wanda ake zargin yana tsare a hannun jami’an tsaro kuma yana “bayar da haɗin kai ga masu bincike kan sunaye da wuraren da sauran mambobin ƙungiyar da ma’adanar makamansu suke.”

Sojoji sun tsananta ƙoƙarin gano tare da kama sauran membobin ƙungiyar da ake zargi da alhakin ayyukan laifuka a yankin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ɗan Ta adda da ake zargin

এছাড়াও পড়ুন:

Nentawe Yilwatda ne zai zama sabon shugaban APC na kasa

Matukar ba a sami sauyin tsare-tsare ba, akwai yiwuwar Ministan Jinkai da Yaki da Talauci, Farfesa Nentawe Yilwatda ya zama sabon shugaban jam’iyyar APC na kasa a yau Alhamis.

Majiyoyi da dama a daren jiya sun shaida wa Aminiya cewa Nentawe ne ke kan gaba a cikin mutanen da ake so su dare shugabancin jam’iyyar mai mulki.

Sai dai a cewar wasu majiyoyin, tsohon Gwamnan Jihar Nasarawa, Sanata Umaru Tanko Almakura shi ma na daga cikin wadanda ake duba yiwuwar ba kujerar.

Sojoji sun kashe Kwamandan Boko Haram Ibn Khalid a Borno NAFDAC ta gano dakin ajiye kayayyaki makare da sinadaran hada bam a Kano

A daidai lokacin da ya rage ’yan sa’o’i gabanin taron Kwamitin Zartarwa na jam’iyyar, majiyoyi da dama sun shaida mana cewa shugabancin jam’iyyar, wanda ya kunshi Shugaban Kasa da Gwamnoni sun yanke shawarar takaita neman wanda zai hau kujerar tsakan Nentawe da Almakura.

Nentawe dai dan asalin jihar Filato ne da ke shiyyar Arewa da Tsakiya, yankin da aka tsara zai fitar da shugaban jam’iyyar kafin daga bisani a nada tsohon Gwamnan Kano, Abdullahi Umar Ganduje, wanda ya ajiye mukaminsa a farkon wannan watan.

To sai dai majiyoyin sun ce an saka sunan Almakura ne a matsayin zabi na biyu.

Tun bayan saukar Ganduje dai ’yan shiyyar Arewa ta Tsakiya ke ta hankoron ganin an dawo da kujerar yankinsu, kasancewar dan cikinsu, wato Sanata Abdullahi Adamu ne ke kanta kafin ya sauka bayan nasarar Shugaba Tinubu a zaben 2023.

Bayanai sun nuna sai da aka yi dogon nazari kafin a yanke shawarar dauko dan yankin kuma Kirista, saboda a hakurkurtar da wadanda zabin Musulmai guda biyu, Tinubu da Kashim, ya bakantawa.

Duk wanda ya yi nasarar dai shi ne zai karbi ragamar da shugabanta na riko na yanzu, Ali Bukar Dalori, wanda mataimakin shugaba ne kafin saukar Ganduje.

Wasu dai na cewa da shi aka kyale ya ci gaba, amma wata majiyar ta ce kasancewarsa daga jiha daya da Kashim sannan kuma Tinubu na so a yi ta ta kare a kan batun shugabancin ya sa dole a zabo wani.

Wata majiyar kuma ta ce, “Tinubu na san wani dan-a-mutun shi ya zama shugaban kamar yadda Abdullahi Adamu ya kasance zamanin Buhari”.

Sauran wadanda a baya aka yi ta rade-radin za su hau kujerar sun hada da Sanata Sani Musa (Neja) da Sanata Salihu Mustapha (Kwara) da Sanata Joshua Dariye (Filato) da Sanata George Akume (Binuwai) da kuma Sanata Abu Ibrahim (Katsina).

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojoji Sun Kwato Makamai Daga Hannun Ƴan Bindiga, Sun Ceto Yaro A Filato
  • Syria: Mutane Da Dama Sun Mutu Da Kuma Jikkata Sanadiyyar Gobara A Rumbun Ajiyar Makamai
  • Hulk Hogan ya mutu yana da shekara 71
  • EFCC Ta Kama Ɗaliban BUK 25 Kan Zargin Aikata Damfara A Intanet A Kano
  • Sojoji sun kashe ’yan ta’adda 95 a Neja, sun ceto mutum 138 da aka sace
  • Nentawe Yilwatda ne zai zama sabon shugaban APC na kasa
  • NAFDAC ta gano dakin ajiye kayayyaki makare da sinadaran hada bam a Kano
  • Gwamna Sule Ya Ƙara Musanta Zargin Kare Ƴan Ta’adda A Nasarawa
  • UNICEF na zargin Gwamnatin Nijeriya da cin zarafin ƙananan yara
  • WHO Ta Buƙaci Isra’ila Ta Saki Ma’aikacinta Da Aka Kama A Gaza