Majalisar Nasarawa Ta Bukaci A Cire Malamai 1000 Daga Aikin Tantancewar Da Ake Yiwa Malamai
Published: 29th, May 2025 GMT
Majalisar dokokin jihar Nasarawa, ta umurci gwamnatin jihar da ta cire sabbin malamai 1000 wadanda ke karbar albashinsu daga aikin tantance malaman da ake yi a jihar.
Mataimakin kakakin majalisar Muhammad Adamu Oyanki, ya yi wannan kiran ne a lokacin da yake karanta kudurin majalisar bayan Daniel Ogazi ya kawo lamarin cikin gaggawa ga al’umma yayin zaman majalisar a lafiya.
Mohammed Adamu Oyanki ya ce malamai 1000 da ke karbar albashin na aiki ne bisa ka’idojin aikin gwamnati don haka ya kamata a cire su daga aikin tantancewar da ake yi a jihar domin samar da zaman lafiya, hadin kai da adalci.
Ya kuma umurci mashawarcin da ke gudanar da aikin tantancewar da ya mayar da wasikun daykar aiki da aka karbo ga malamai 1000 da ke kan lissafin albashin gwamnati nan take.
A cewarsa, wannan abin bakin ciki ne kuma abin takaici ne, wadannan malamai 1000 sun samu aikin yi yadda ya kamata kuma suna karbar albashin watanni 9.
“Kudirin da majalisar ta yi shi ne, muna godiya ga mai girma Gwamna Abdullahi Sule bisa yadda ya dauki malamai aikin yi domin kara inganta harkar ilimi da kuma rage rashin aikin yi a jihar.
“Muna kuma umurtar mai ba da shawara da ya mayar wa malamai 1000 wasikun daukar da aka karbo nan take sannan su ci gaba da koyarwa, a biya su albashi” Inji shi.
“Kada wata hukuma ta dauki laifin wani, malamai 1000, kowa ya san ba su da laifi domin sun bi duk hanyoyin da suka dace don haka kada a ci zarafinsu, abin da muke yi shi ne kare gwamnati da doka.” Ya kara da cewa.
Mataimakin shugaban majalisar ya kuma kafa kwamiti na mutum shida wanda Daniel Ogazi zai jagoranta tare da shugaban kwamitin ilimi Abel Yakubu Bala tare da Luka Iliya Zhekaba a matsayin Sakatare da Barr. Esson Mairiga, Solomon Akwashiki da Muhammed Garba Isimbabi a matsayin membobi don kawo duk masu laifin da suka sayar da wasikun daukar aiki ga ’yan asalin jihar domin su samu.
“Wannan kwamiti zai kasance karkashin jagorancin Hon Daniel Ogazi tare da Hon. Luka Iliya Zhekaba, shugaban marasa rinjaye a matsayin sakataren kwamitin.
“Sauran mambobin sun hada da Hon. Solomon Yakubu Akwashiki, Hon. Mohammed Garba Isimbabi da Hon. Barr. Esson Mairiga” inji shi.
Mataimakin shugaban majalisar ya yi kira ga gwamna Abdullahi Sule da ya yi adalci tare da tausaya wa sauran malamai sama da 2000 da ba a biya su albashi ba.
COV/Aliyu Muraki/Lafia.
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Majalisar Dokoki nasarawa
এছাড়াও পড়ুন:
Dan Majalisar Jema’a/Sanga, Daniel Amos, Ya Koma Jam’iyyar APC
Harkokin siyasa na Kudancin Kaduna ya dauki wani salo yayin da dan majalisar da ke wakiltar mazabar Jema’a/Sanga a majalisar tarayya, Hon. Dan Amos, ya sanar da komawarsa jam’iyyar APC mai mulki zuwa jam’iyyar PDP, yana mai cewa ya dauki wannan mataki ne domin ya hada kai da gwamnatocin jiha da na tarayya don cigaban yankin.
Yayin da yake jawabi ga manema labarai a Kafanchan kafin karbar sa a hukumance tare da Sanata Marshall Katung, Amos ya bayyana cewa wannan mataki ya biyo bayan dogon shawarwari da aka yi da shugabannin al’umma, kungiyoyin addini, kwararru da kuma sarakunan gargajiya a fadin mazabarsa.
Ya ce jam’iyyar PDP, wacce a da take da karfi sosai a Kaduna, ta ragu saboda rikice-rikicen cikin gida da suka dade suna faruwa, wanda hakan ya janyo ficewar mambobi da kuma rasa goyon bayan talakawa a fadin kasa.
“Mun dauki lokaci muna tattaunawa da mutane a matakai daban-daban – daga tsarin jam’iyya zuwa kungiyoyin addini da na kwararru – kuma abin da muka cimma shine, don amfanin jama’armu, ya dace mu nemi wata madogara ta daban,”
“Ya zama sauki mu shiga APC saboda muna ganin irin kokarin da Shugaba Bola Ahmed Tinubu da Gwamna Uba Sani ke yi wajen hada yankin Kudancin Kaduna cikin shirin cigaba da ci gaba da kasa.” in ji Amos.
Dan majalisar ya yaba wa Shugaba Tinubu bisa nadin ɗan asalin yankin, Janar Christopher Musa, a matsayin Babban Hafsan Tsaro (CDS) da kuma amincewa da a kafa Jami’ar Kimiyyar Aiki ta Tarayya da Asibitin Tarayya (Federal Medical Centre) a yankin.
Ya kuma gode wa Gwamna Uba Sani saboda gudanar da mulki cikin hadin kai, gina ababen more rayuwa, da bude kofa ga kowa, wanda ya ce ya karfafa zumunci da bai wa kowane bangare na jihar damar shiga.
“Shugaban kasa da gwamna suna nuna shugabanci na hada kan jama’a. Wannan ya sa muka ga dacewar mu hade da su domin mu samu karin cigaba a yankinmu,” in ji Amos.
Amos ya karyata jita-jitar cewa ya koma APC don son kai ko muradin siyasa, yana mai cewa wannan mataki ne na Allah da kuma na amfanin jama’ar Kudancin Kaduna.
“Ba don bukatar kaina ba ne, amma don mu tabbatar da yankinmu ya ci gajiyar dimokuradiyya. Ina da yakinin cewa tarihi zai tuna da mu bisa wannan mataki na jarumta da muka dauka,” ya kara da cewa.
Dan majalisar, wanda shi ne Shugaban Kwamitin Ayyukan Majalisa, ya tabbatar wa mazaunar mazabarsa cewa komawarsa APC ba za ta canza manufarsa ta kyakkyawan wakilci ba, yana mai cewa ya shiga jam’iyyar mai mulki ne don kara daraja, ba don kawo rarrabuwar kawuna ba.
Ya bayyana fatan cewa da hadin kai tsakanin jama’a da gwamnati, Kudancin Kaduna zai ci gaba da samun cigaba a bangaren ababen more rayuwa, ilimi, da tsaro.
An shirya taron karbar Amos, Sanata Katung, da sauran wadanda suka koma daga PDP zuwa APC a ranar 1 ga Nuwamba a Kafanchan, kuma manyan baki da ake sa ran halarta sun hada da Mataimakin Shugaban Kasa, Kashim Shettima, Kakakin Majalisar Wakilai, Rt. Hon. Tajudeen Abbas, da kuma shugabannin jam’iyyar APC daga fadin kasar nan.
Radio Nigeria ta ruwaito cewa wannan sauyin jam’iyya ya nuna babban sauyi a siyasar jihar Kaduna, wanda ya kawo karshen rinjayen PDP da ta yi sama da shekaru 25 a Kudancin jihar.
Daniel Karlmax