Majalisar dokokin jihar Nasarawa, ta umurci gwamnatin jihar da ta cire sabbin malamai 1000 wadanda ke karbar albashinsu daga aikin tantance malaman da ake yi a jihar.

 

Mataimakin kakakin majalisar Muhammad Adamu Oyanki, ya yi wannan kiran ne a lokacin da yake karanta kudurin majalisar bayan Daniel Ogazi ya kawo lamarin cikin gaggawa ga al’umma yayin zaman majalisar a lafiya.

 

Mohammed Adamu Oyanki ya ce malamai 1000 da ke karbar albashin na aiki ne bisa ka’idojin aikin gwamnati don haka ya kamata a cire su daga aikin tantancewar da ake yi a jihar domin samar da zaman lafiya, hadin kai da adalci.

 

Ya kuma umurci mashawarcin da ke gudanar da aikin tantancewar da ya mayar da wasikun daykar aiki da aka karbo ga malamai 1000 da ke kan lissafin albashin gwamnati nan take.

 

A cewarsa, wannan abin bakin ciki ne kuma abin takaici ne, wadannan malamai 1000 sun samu aikin yi yadda ya kamata kuma suna karbar albashin watanni 9.

 

“Kudirin da majalisar ta yi shi ne, muna godiya ga mai girma Gwamna Abdullahi Sule bisa yadda ya dauki malamai aikin yi domin kara inganta harkar ilimi da kuma rage rashin aikin yi a jihar.

 

 

“Muna kuma umurtar mai ba da shawara da ya mayar wa malamai 1000 wasikun daukar da aka karbo nan take sannan su ci gaba da koyarwa, a biya su albashi” Inji shi.

 

“Kada wata hukuma ta dauki laifin wani, malamai 1000, kowa ya san ba su da laifi domin sun bi duk hanyoyin da suka dace don haka kada a ci zarafinsu, abin da muke yi shi ne kare gwamnati da doka.” Ya kara da cewa.

 

Mataimakin shugaban majalisar ya kuma kafa kwamiti na mutum shida wanda Daniel Ogazi zai jagoranta tare da shugaban kwamitin ilimi Abel Yakubu Bala tare da Luka Iliya Zhekaba a matsayin Sakatare da Barr. Esson Mairiga, Solomon Akwashiki da Muhammed Garba Isimbabi a matsayin membobi don kawo duk masu laifin da suka sayar da wasikun daukar aiki ga ’yan asalin jihar domin su samu.

 

“Wannan kwamiti zai kasance karkashin jagorancin Hon Daniel Ogazi tare da Hon. Luka Iliya Zhekaba, shugaban marasa rinjaye a matsayin sakataren kwamitin.

 

“Sauran mambobin sun hada da Hon. Solomon Yakubu Akwashiki, Hon. Mohammed Garba Isimbabi da Hon. Barr. Esson Mairiga” inji shi.

 

Mataimakin shugaban majalisar ya yi kira ga gwamna Abdullahi Sule da ya yi adalci tare da tausaya wa sauran malamai sama da 2000 da ba a biya su albashi ba.

COV/Aliyu Muraki/Lafia.

 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Majalisar Dokoki nasarawa

এছাড়াও পড়ুন:

Mai Martaba Sarkin Kazaure Ya Bukaci Alhazai Su Yi Addu’o’i Na Musamman Ga Kasarsu

An bukaci Maniyyatan Jihar Jigawa su yi addu’o’i ga jihar da kasa Najeriya domin samun zaman lafiya a yayin zaman su a kasa Mai tsarki.

 

Amirul Hajj na Jihar, Mai Martaba Sarkin Kazaure Dr Najib Hussaini Adamu yayi wannan kiran a lokacin da yake jawabi ga Maniyyatan Jihar a Kasar Saudi Arabia.

 

Amirul hajjin ya hori Maniyyatan da suyi addu’a tare da karkatar da zukatansu ga dabi’u nagari, inda ya bayyana cewar canza dabi’u tare da komawa ga Allah ne kadai hanyar da za’a bi don magance matsalolin da suka addabi kasa Najeriya.

 

Dr Najib Hussaini Adamu, yace Allah ya albarkaci Jihar Jigawa da ni’imomi da dama, a don haka ya bukace su da su kara karfafa addu’o’i.

 

Kazalika, Sarkin ya kuma yabawa tallafin da gwamnati jihar ta bayar domin tabbatuwar aiwatar da hajjin bana.

 

A don haka, yayi kira ga Maniyyatan da su yi wa gwamnatin Jihar jigawan addu’a.

 

Ya kuma bukace su da su zama masu bin dokokin kasar saudiyya, yana mai horan su da su zamo masu tsafta kuma  jakadu nagari a ko ina musamman a zaman Muna.

 

Mai Martaba ya kuma kara jan hankulansu da su zama abin misali a wajen kula da tsaftar muhalli yana mai fatan Allah yasa ayi ibada lafiya a koma gida lafiya.

 

Usman Mohammad Zaria

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Majalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince Da Dokokin Ilimin Noma da Gyaran Kotunan Gargajiya
  • Majalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince Da Sabbin Kwamishinoni Biyu
  • MDD Ta Gudanar Da Bikin Ranar Tunawa Da Dakarun Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Duniya Ta 2025
  • Kasar Iran, Da Kasashen Kungiyar BRICS Sun Gudanar Da Taro Kan Harkokin Tsaro A Mosco
  • Gwamnatin Gombe ta rattaba hannu kan kwangilar biliyan 48 na aikin zaizayar Kasa
  • Sojoji sun halaka mayakan ISWAP da dama a Borno
  • Wata Hajiya ‘Yar Nijeriya Mai Shekaru 75 Ta Rasu A Saudiyya Yayin Aikin Hajji
  • Mai Martaba Sarkin Kazaure Ya Bukaci Alhazai Su Yi Addu’o’i Na Musamman Ga Kasarsu
  • An Sake Zaben Qalibof A Matsayin Shugaban Majalisar Dokokin Kasar Iran