Majalisar dokokin jihar Nasarawa, ta umurci gwamnatin jihar da ta cire sabbin malamai 1000 wadanda ke karbar albashinsu daga aikin tantance malaman da ake yi a jihar.

 

Mataimakin kakakin majalisar Muhammad Adamu Oyanki, ya yi wannan kiran ne a lokacin da yake karanta kudurin majalisar bayan Daniel Ogazi ya kawo lamarin cikin gaggawa ga al’umma yayin zaman majalisar a lafiya.

 

Mohammed Adamu Oyanki ya ce malamai 1000 da ke karbar albashin na aiki ne bisa ka’idojin aikin gwamnati don haka ya kamata a cire su daga aikin tantancewar da ake yi a jihar domin samar da zaman lafiya, hadin kai da adalci.

 

Ya kuma umurci mashawarcin da ke gudanar da aikin tantancewar da ya mayar da wasikun daykar aiki da aka karbo ga malamai 1000 da ke kan lissafin albashin gwamnati nan take.

 

A cewarsa, wannan abin bakin ciki ne kuma abin takaici ne, wadannan malamai 1000 sun samu aikin yi yadda ya kamata kuma suna karbar albashin watanni 9.

 

“Kudirin da majalisar ta yi shi ne, muna godiya ga mai girma Gwamna Abdullahi Sule bisa yadda ya dauki malamai aikin yi domin kara inganta harkar ilimi da kuma rage rashin aikin yi a jihar.

 

 

“Muna kuma umurtar mai ba da shawara da ya mayar wa malamai 1000 wasikun daukar da aka karbo nan take sannan su ci gaba da koyarwa, a biya su albashi” Inji shi.

 

“Kada wata hukuma ta dauki laifin wani, malamai 1000, kowa ya san ba su da laifi domin sun bi duk hanyoyin da suka dace don haka kada a ci zarafinsu, abin da muke yi shi ne kare gwamnati da doka.” Ya kara da cewa.

 

Mataimakin shugaban majalisar ya kuma kafa kwamiti na mutum shida wanda Daniel Ogazi zai jagoranta tare da shugaban kwamitin ilimi Abel Yakubu Bala tare da Luka Iliya Zhekaba a matsayin Sakatare da Barr. Esson Mairiga, Solomon Akwashiki da Muhammed Garba Isimbabi a matsayin membobi don kawo duk masu laifin da suka sayar da wasikun daukar aiki ga ’yan asalin jihar domin su samu.

 

“Wannan kwamiti zai kasance karkashin jagorancin Hon Daniel Ogazi tare da Hon. Luka Iliya Zhekaba, shugaban marasa rinjaye a matsayin sakataren kwamitin.

 

“Sauran mambobin sun hada da Hon. Solomon Yakubu Akwashiki, Hon. Mohammed Garba Isimbabi da Hon. Barr. Esson Mairiga” inji shi.

 

Mataimakin shugaban majalisar ya yi kira ga gwamna Abdullahi Sule da ya yi adalci tare da tausaya wa sauran malamai sama da 2000 da ba a biya su albashi ba.

COV/Aliyu Muraki/Lafia.

 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Majalisar Dokoki nasarawa

এছাড়াও পড়ুন:

An kama tsohon minista kan zargin kisan kai domin tsafi a Nijar

Antoni Janar na Kotun Ɗaukaka Ƙara da ke birnin Yamai a Nijar, ya bayyana cewa an kama tsohon Ministan Harkokin Waje, Ibrahim Yacoubou, bisa zargin hannunsa a cikin wata aika-aika ta kisan kai domin yin tsafi.

A cewar Maazou Oumarou, lamarin ya samo asali ne daga wani binciken ’yan sanda da aka fara gudanarwa tun a ranar 29 ga Yuli, 2025.

KEDCO ya ƙaryata asibitin AKTH kan mutuwar majinyata saboda ɗauke wuta Dole sai mun tantance wa’azi kafin a yi —Gwamnan Neja

Ya bayyana cewa, an soma gudanar da binciken ne dangane da yunƙurin kisa a wani yanki da ke wajen birnin Yamai, lamarin da ya kai ga cafke ababen zargin a garin Dosso.

Wani mutum mai suna Mahamadou Noura ne ya bayyana cewa shi ne ya yi yunƙurin kisan, tare da wasu kashe-kashe guda shida da ya aiwatar a baya, bisa umarnin wasu mutane, ciki har da tsohon ministan Ibrahim Yacoubou.

Mutumin ya shaida wa mahukunta cewa ya aikata hakan ne domin yin tsafi da gawarwakin, a madadin wasu mutane da suka haɗa da: Issa Ali Maiga da Ismael Morou Karama da Elhadji Bilya da kuma Issa Seybou Hama.

TRT ya ruwaito cewa tuni dai an cafke duk ababen zargin, yayin da Kotun Ɗaukaka Ƙarar ta umurci ’yan sanda da su ci gaba da bincike tare da ɗaukar ƙarin matakan da za su tabbatar da gaskiya.

Sanarwar ta ce: “Manufar wannan mataki na shari’a ita ce a tattara cikakken rahoto da ke ƙunshe da dukkan abubuwan da suka faru, sannan a miƙa shi ga ɓangaren gurfanarwa.”

Mai shigar da ƙara a ɓangaren gwamnati ya ce, la’akari da girman wannan lamari, wajibi ne a gudanar da bincike cikin gaggawa.

Haka kuma ya buƙaci al’umma da su mutunta ’yancin kotu tare da bayar da cikakken goyon baya domin fayyace gaskiya.

Ana iya tuna cewa, Ibrahim Yacoubou na daga cikin manyan jami’an da aka kama bayan juyin mulkin Nijar na ranar 26 ga Yuli, 2023, sai dai daga bisani an ba shi beli na wucin gadi a cikin watannin baya.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Majalisar Dokokin Jihar Jigawa Ta Kammala Ziyarar Yini 3 A Ma’aikatar Kananan Hukumomin Jihar
  • Tinubu Ya Janye Dokar Ta-baci A Jihar Rivers
  • An tattauna yadda za a inganta walwalar malamai a Gombe
  • Guterres: Jerin Shawarwarin Da Sin Ta Gabatar Sun Cika Ka’idar Kundin Tsarin Majalisar Dinkin Duniya
  • Gwamna Namadi Ya Taya Malaman Makarantu Da Suka Yi Fice A Jihar Murna
  • Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu
  • Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 
  • Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 
  • An kama tsohon minista kan zargin kisan kai domin tsafi a Nijar
  • Ɗangote zai gina ɗakunan kwanan ɗalibai 250  a Jami’ar Ilorin