Majalisar dokokin jihar Nasarawa, ta umurci gwamnatin jihar da ta cire sabbin malamai 1000 wadanda ke karbar albashinsu daga aikin tantance malaman da ake yi a jihar.

 

Mataimakin kakakin majalisar Muhammad Adamu Oyanki, ya yi wannan kiran ne a lokacin da yake karanta kudurin majalisar bayan Daniel Ogazi ya kawo lamarin cikin gaggawa ga al’umma yayin zaman majalisar a lafiya.

 

Mohammed Adamu Oyanki ya ce malamai 1000 da ke karbar albashin na aiki ne bisa ka’idojin aikin gwamnati don haka ya kamata a cire su daga aikin tantancewar da ake yi a jihar domin samar da zaman lafiya, hadin kai da adalci.

 

Ya kuma umurci mashawarcin da ke gudanar da aikin tantancewar da ya mayar da wasikun daykar aiki da aka karbo ga malamai 1000 da ke kan lissafin albashin gwamnati nan take.

 

A cewarsa, wannan abin bakin ciki ne kuma abin takaici ne, wadannan malamai 1000 sun samu aikin yi yadda ya kamata kuma suna karbar albashin watanni 9.

 

“Kudirin da majalisar ta yi shi ne, muna godiya ga mai girma Gwamna Abdullahi Sule bisa yadda ya dauki malamai aikin yi domin kara inganta harkar ilimi da kuma rage rashin aikin yi a jihar.

 

 

“Muna kuma umurtar mai ba da shawara da ya mayar wa malamai 1000 wasikun daukar da aka karbo nan take sannan su ci gaba da koyarwa, a biya su albashi” Inji shi.

 

“Kada wata hukuma ta dauki laifin wani, malamai 1000, kowa ya san ba su da laifi domin sun bi duk hanyoyin da suka dace don haka kada a ci zarafinsu, abin da muke yi shi ne kare gwamnati da doka.” Ya kara da cewa.

 

Mataimakin shugaban majalisar ya kuma kafa kwamiti na mutum shida wanda Daniel Ogazi zai jagoranta tare da shugaban kwamitin ilimi Abel Yakubu Bala tare da Luka Iliya Zhekaba a matsayin Sakatare da Barr. Esson Mairiga, Solomon Akwashiki da Muhammed Garba Isimbabi a matsayin membobi don kawo duk masu laifin da suka sayar da wasikun daukar aiki ga ’yan asalin jihar domin su samu.

 

“Wannan kwamiti zai kasance karkashin jagorancin Hon Daniel Ogazi tare da Hon. Luka Iliya Zhekaba, shugaban marasa rinjaye a matsayin sakataren kwamitin.

 

“Sauran mambobin sun hada da Hon. Solomon Yakubu Akwashiki, Hon. Mohammed Garba Isimbabi da Hon. Barr. Esson Mairiga” inji shi.

 

Mataimakin shugaban majalisar ya yi kira ga gwamna Abdullahi Sule da ya yi adalci tare da tausaya wa sauran malamai sama da 2000 da ba a biya su albashi ba.

COV/Aliyu Muraki/Lafia.

 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Majalisar Dokoki nasarawa

এছাড়াও পড়ুন:

Wata Kungiyar Ta Bukaci Shugaban Kasa Ya Cika Alkwarin Marigayi Shugaba Buhari Game Da Shehu Usman Aliyu Shagari

A wani roko da wata kungiya da aka fi sani da Sokoto Heritage Reloaded Initiative ta yi kira ga shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu da ya cika alkawarin da tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari ya dauka a lokacin wata ziyarar aiki da ya kai a jihar.

 

An yi wannan roko ne a yayin wani taron manema labarai da aka gudanar a jihar Sokoto, inda shugaban kungiyar Farfesa Uthman Abdulqadir, ya jaddada muhimmancin girmama abubuwan da Shagari ya bari.

 

Ya tuna cewa shugaba Buhari ya yi wannan alkawari ne a ziyarar da ya kai Sokoto.

 

Farfesa Uthman ya bayyana irin rawar da Shehu Shagari yake takawa wajen ciyar da ilimi gaba a Najeriya, inda ya bayyana cewa ya taka rawa wajen aza harsashin kafa Budaddiyar Jami’ar Nijeriya.

 

Ya bayyana Shagari ba wai kawai shugaba ba, a’a a matsayin alama ce ta tawali’u, rikon amana da kishin kasa, mutumin da ya sadaukar da rayuwarsa wajen yi wa kasarsa hidima.

 

Farfesa Uthman ya bayyana kwarin guiwar cewa shugaba Tinubu, wanda ya shahara da mutunta shuwagabannin kasa da jajircewar hadin kai, zai gane muhimmancin tunawa Shehu Shagari.

 

Ya yi imanin cewa wannan aikin zai bayyana a fili karara Tinubu a matsayin jagora mai girmama kimar tawali’u, hidima, da kishin kasa.

 

Farfesa Uthman ya jaddada cewa sanyawa wurare sunayen Dattijai ba karamin alfanu ne ga rayuwa jama’ar ba.

 

Ya bayyana shi a matsayin muhimmin kayan aiki don ilimi, zaburarwa, da kuma kiyaye dabi’un da suka dace da al’ummomin yanzu da na gaba.

 

NASIR MALAL

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Natasha za ta sake komawa kotu kan hana ta shiga harabar majalisa
  • Gwamna Namadi Ya Sanya Hannu Kan Dokar Kafa Hukumar Hisba Ta Jihar Jigawa
  • Zhao Leji Da Wang Huning Sun Gana Da Shugaban Majalisar Dattijan Kasar Madagascar
  • Majalisar Dokokin Jihar Jigawa Ta Kai Ziyarar Gani Da Ido Kirikasamma
  • HOTUNA: An ƙaddamar da aikin sabunta ginin Majalisar Dokokin Bauchi
  • Sin Ta Samar Da Karin Guraben Aikin Yi Miliyan 6.95 A Rabin Farko Na Bana
  • Asibitin ATBUTH za ta fara gwajin rigakafin zazzaɓin Lassa
  • Gwamnatin Zamfara Ta Kira Babban Taron Tsaro Tare Da Bayyana Sabbin Dabaru Na Yakar ‘Yan Bindiga.
  • Wata Kungiyar Ta Bukaci Shugaban Kasa Ya Cika Alkwarin Marigayi Shugaba Buhari Game Da Shehu Usman Aliyu Shagari
  • Mataimakiyar Shugaban Majalisar Dinkin Duniya Ta Jinjinawa Gwamnan Kano Bisa Ayyukan Cigaban Jihar