Gwamnatin Kano ta haramta liƙa hotuna ko rubutu marasa ma’ana a A-Daidaita-Sahu
Published: 31st, May 2025 GMT
Hukumar Tace Fina-finai ta Jihar Kano ta sanar da haramta rubuce-rubuce ko liƙa hotuna “marasa ma’ana” ko na batsa a kan baburan A-Saidaita-Sahu a fadin jihar.
Wannan mataki, wanda Shugaban Hukumar, Abba El-Mustapha ya jagoranta, yana da nufin tabbatar da ɗa’a da kuma tabbatar da cewa abubuwan da ake nunawa a bainar jama’a sun dace da ƙa’idojin hukumar.
A cewar Abdullahi Sani Sulaiman, Jami’in Hulɗa da Jama’a na hukumar, an ɗauki wannan mataki ne a sakamakon ƙorafe-ƙorafen al’ummaar Kano game da yadda masu A-Daidaita-Sahu sahu ke ado da hotuna da rubuce-rubuce masu ban haushi a bainar jama’a.
Abba El-Mustapha ya jaddada cewa dokar da ta kafa Hukumar ta ba ta cikakken iko don sa ido da gurfanar da masu laifi. Don tabbatar da bin doka, El-Mustapha ya jagoranci wata tawaga ta musamman a wani gangamin wayar da kai zuwa manyan tituna a Kano, ciki har da Titin Maiduguri, Titin Zaria, da Titin Sani Marshal.
Mai neman aiki ya suma bayan matarsa ta haifi ’yan uku Mutanen da suka mutu a ambaliyar Neja sun ƙaru zuwa 88 —NSEMAA yayin aikin, ya nanata cewa hukumar ba za ta yi ƙasa a gwiwa ba wajen hukunta duk wanda aka samu da laifin karya ka’idojinta, ba tare da la’akari da matsayinsa ba.
El-Mustapha ya ƙara da cewa, bisa ga umarnin hukumar, duk wani aikin adabi ko na fasaha dole ne a miƙa shi ga Hukumar ta tantance shi kafin a fitar da shi ga jama’a.
Ya yi kira ga al’umma da su ba hukumar cikakken goyon baya da haɗin kai don ci gaban Jihar Kano.
Wannan sabon mataki ya biyo bayan wani shiri na wayar da kai da aka yi a baya inda hukumar ta tattauna da fiye da masu adaidaita sahu 20, inda ta yi musu gargaɗi game da sabbin dokokin. Hukumar ta bayyana cewa sabuwar dokar ta fara aiki cikakke.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: El Mustapha ya
এছাড়াও পড়ুন:
NAHCON ta kammala jigilar maniyyata aikin hajjin 2025
Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta kammala jigilar maniyyatan Najeriya zuwa ƙasar Saudiyya domin gudanar da aikin hajjin shekarar 2025.
Da yake jawabi ga manema labarai a filin jirgin sama na Nnamdi Azikiwe da ke Abuja kafin jirgin maniyyatan ya tashi zuwa Saudiyya, Shugaban Hukumar NAHCON, Farfesa Abdullahi Saleh Usman, ya ce aikin Hajjin bana ya samu nasarori da dama da suka nuna ci gaba da inganta aikin hajjin Nijeriya.
NDLEA ta kama maniyyata aikin hajji ɗauke da hodar iblis ’Yan bindiga sun kashe makiyaya 2, sun sace shanu 320 a KadunaYa ce, an yi jigilar maniyyata 41,568 ta jiragen sama 105.
Hakan na zuwa ne a daidai lokacin da ya nuna matuƙar godiya ga shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu da mataimakin shugaban ƙasa, Sanata Kashim Shettima bisa gagarumin goyon bayan da suka bayar wajen ganin an gudanar da aikin Hajjin 2025 cikin nasara.
A cewarsa, duk da cewa aikin jigilar jirage ba abu ne mai sauƙi ba, tare da haɗin gwiwar masu ruwa da tsaki, hukumar ta samu nasarar kammala aikin.
Shugaban Hukumar NAHCON ya bayyana cewa, akwai ƙalubale a yayin aikin jigilar jiragen amma tare da haɗin gwiwar hukumar ta samu nasarar cimma burinta na ganin duk wani mahajjatan Najeriya ya tafi ƙasa mai tsarki tare da kula da su yadda ya kamata.
“Yayin da muke rufe shirin jigilar jirage zuwa aikin Hajjin 2025 na bana daga kason jihar, wannan lokaci ne mai matuƙar muhimmanci a gare mu baki ɗaya domin hakan na nufin mun samu nasarar kwashe dubban maniyyatanmu cikin ‘yan makonni.
“Ba abu ne mai sauƙi ba, amma da kyakkyawan tsari, bayan taimakon Allah Maɗaukakin Sarki da haɗin gwiwar da muka yi, mun kammala aiki cikin nasara, Alhamdulillah.