Gwamnatin Kano ta haramta liƙa hotuna ko rubutu marasa ma’ana a A-Daidaita-Sahu
Published: 31st, May 2025 GMT
Hukumar Tace Fina-finai ta Jihar Kano ta sanar da haramta rubuce-rubuce ko liƙa hotuna “marasa ma’ana” ko na batsa a kan baburan A-Saidaita-Sahu a fadin jihar.
Wannan mataki, wanda Shugaban Hukumar, Abba El-Mustapha ya jagoranta, yana da nufin tabbatar da ɗa’a da kuma tabbatar da cewa abubuwan da ake nunawa a bainar jama’a sun dace da ƙa’idojin hukumar.
A cewar Abdullahi Sani Sulaiman, Jami’in Hulɗa da Jama’a na hukumar, an ɗauki wannan mataki ne a sakamakon ƙorafe-ƙorafen al’ummaar Kano game da yadda masu A-Daidaita-Sahu sahu ke ado da hotuna da rubuce-rubuce masu ban haushi a bainar jama’a.
Abba El-Mustapha ya jaddada cewa dokar da ta kafa Hukumar ta ba ta cikakken iko don sa ido da gurfanar da masu laifi. Don tabbatar da bin doka, El-Mustapha ya jagoranci wata tawaga ta musamman a wani gangamin wayar da kai zuwa manyan tituna a Kano, ciki har da Titin Maiduguri, Titin Zaria, da Titin Sani Marshal.
Mai neman aiki ya suma bayan matarsa ta haifi ’yan uku Mutanen da suka mutu a ambaliyar Neja sun ƙaru zuwa 88 —NSEMAA yayin aikin, ya nanata cewa hukumar ba za ta yi ƙasa a gwiwa ba wajen hukunta duk wanda aka samu da laifin karya ka’idojinta, ba tare da la’akari da matsayinsa ba.
El-Mustapha ya ƙara da cewa, bisa ga umarnin hukumar, duk wani aikin adabi ko na fasaha dole ne a miƙa shi ga Hukumar ta tantance shi kafin a fitar da shi ga jama’a.
Ya yi kira ga al’umma da su ba hukumar cikakken goyon baya da haɗin kai don ci gaban Jihar Kano.
Wannan sabon mataki ya biyo bayan wani shiri na wayar da kai da aka yi a baya inda hukumar ta tattauna da fiye da masu adaidaita sahu 20, inda ta yi musu gargaɗi game da sabbin dokokin. Hukumar ta bayyana cewa sabuwar dokar ta fara aiki cikakke.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: El Mustapha ya
এছাড়াও পড়ুন:
Hukumar Kashe Gobara Ta Jihar Kwara Ta Taimaka Wajen Hana Lalacewar Wani Bene A Ilorin
Hukumar kashe gobara ta jihar Kwara, ta ce ta ceto wani bene mai hawa biyu daga rugujewa gaba daya sakamakon wata gobara da ta tashi a garin Ilorin.
Kakakin hukumar kashe gobara ta jihar Kwara, Hassan Adekunle ya bayyana haka a cikin wata sanarwa da ya fitar inda y ace gobara da ta tashi a hanyar Muritala Muhammed, daura da Cocin C & S, Ilorin.
A cewarsa da isar su, ma’aikatan kashe gobara sun gano cewa wani gini mai hawa biyu da ya kunshi dakuna 8 da shaguna 10 na fuskantar barazana. Ya bayyana cewa, ta hanyar daukar mataki cikin gaggawa da hadin kai, jami’an kashe gobara sun samu nasarar shawo kan gobarar yadda ya kamata, tare da hana yaduwarta zuwa gine-ginen da ke kewaye, inda ta kara da cewa a sakamakon haka, daki daya ne lamarin ya shafa.
Ya ce binciken farko ya nuna cewa wutar lantarki ce dalilin ta tashin gobarar.
Da yake mayar da martanin Daraktan Hukumar Kashe Gobara ta Jihar Kwara Prince Falade Olumuyiwa, ya bukaci jama’a da su kasance cikin shiri da kiyaye lafiya a gidajensu da wuraren kasuwancinsu.
REL/ALI MUHAMMAD RABIU