Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp.

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Barau

এছাড়াও পড়ুন:

Za A Horas Da Jami’an Tsaron Sakkwato, Kaduna Da Benue Sabbin Dabarun Aiki

Wata kungiya mai zaman kanta mai suna Kukah Centre ta ce ta kuduri aniyar horar da jami’an tsaro a jihohin Sokoto, Kaduna da Benue.

 

Daraktan Cibiyar Kukah Reverend Father Atta Barkindo, wanda ya bayyana hakan ya ce an dauki matakin ne domin taimakawa kokarin gwamnatin tarayya wajen magance matsalolin tsaro da ke ci gaba da addabar al’ummar kasar.

 

Reverend Father Atta Barkindo, ya jaddada cewa an shirya horon ne domin inganta tsaro a tsakanin al’umma a cikin dimbin kalubalen da jihohi da dama ke fama da su a fadin kasar nan.

 

Ya kuma bayyana bukatar kafa jami’an tsaro na Jihohi su samar da ingantattun tsare-tsare don tabbatar da samar da ayyuka masu inganci.

 

Shima da yake jawabi, jami’in kula da ayyukan cibiyar Kukah, Terseer Bamber, ya yi nuni da cewa, wasu daga cikin jami’an tsaron jihar sun fuskanci tuhume-tuhume na take hakkin dan Adam da cin zarafin mata.

 

Ya jaddada mahimmancin magance wadannan matsalolin a matsayin wani abin da ake bukata domin samun ci gaba mai dorewa a Najeriya.

 

Ana aiwatar da aikin horon ne tare da haɗin gwiwar Cibiyar Kukah, Ci gaban Ƙasashen Duniya na Birtaniya, da Tetra Tech International Development.

 

A nasa jawabin, Mai Alfarma Sarkin Musulmi Muhammad Sa’ad Abubakar wanda Sarkin Yakin Gagi, Hakimin Gagi Alhaji Sani Umar Jabbi ya wakilta, ya yi maraba da shirin inda ya bayyana cewa Sarkin Musulmi a shirye yake ya tallafa wa duk wani kokari da zai taimaka kai tsaye wajen samar da zaman lafiya da ci gaban kasa.

 

 

Ya bukaci gwamnatocin jihohi da su ba da fifiko wajen wanzar da zaman lafiya da hadin kai, yana mai korafin cewa kalubalen tsaro ya yi matukar tasiri ga zaman lafiya da ci gaban tattalin arzikin kasar.

 

Rediyon Najeriya ya rawaito cewa taron ya samu halartar wakilai daga jami’an ‘yan sanda, da Civil Defence, masu aikin shari’a, ‘yan majalisar dokoki, da kuma shugabannin gargajiya, inda ya bayyana tsarin hadin gwiwa na inganta tsaro a Najeriya.

 

Nasir Malali/Sakkwato

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shirin Sabunta Fata Na Tinubu Yana Samar da Damarmakin Cigaba — Minista
  • Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL
  • Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe
  • Dangote Ya Yaba Wa Tinubu Kan Samar Da Ababen More Rayuwa A Nijeriya
  • Jami’ar Tarayya ta Gashuwa za ta ba matar Tinubu digirin girmamawa
  • An Yi Hasashen Karuwar Tattalin Arzikin Kasar Sin Za Ta Zarce Yuan Tiriliyan 35 Tsakanin 2021 Zuwa 2025
  • Jami’an tsaro sun hallaka ’yan bindiga 30 a Katsina
  • Mai Tsoron Ta Mutu, Shi Yake Maho
  • Matar tsohon Gwamnan Adamawa ta sauya sheka daga PDP zuwa ADC
  • Za A Horas Da Jami’an Tsaron Sakkwato, Kaduna Da Benue Sabbin Dabarun Aiki