Sojojin Yahudawa sun Kashe Wani Matashi A Yankin Yamma Da Kogin Jordan
Published: 27th, May 2025 GMT
Wani bafalasdine ya rasa ransa, bayan da harsasai da sojojin yahudawa suka cilla masa a garin Ariha na yankin yamma da kogin Jordan sun fada a kansa.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto kamfanin dillancin labaran Falasdinawa WAFA ya na fadar haka a yau Talata, ya kuma kara da cewa Mohammed Yahya Asi Jalaytah ya yi shahada ne bayan da albarusan da sojojin suka cilla masa sun fada a kansa sun kuma ji masa munanan raunuka.
Labarin ya kara da cewa bayan tsakiyar dare ne sojojin yahudawan suka soma barin wuta da bindigogi da kuma jefa hayaki mai sa hawaye a kan Falasdinawa a garin Ariha, Inda albarusai suka sami Asi Jalaita suka kuma kasashe shi. WAFA ya ce an garzaya da shi zuwa asbiti amma likitoci suka tabbatar da shahadarsa..
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
‘Yar Majalisar Dokokin Ireland Ta Yi Suka Kan Shugabannin Turai Tare Da Neman Afuwa Daga Falasdinawa
‘Yar majalisar dokokin Ireland ta yi kakkausar suka kan shugabannin Turai tare da neman afuwa daga Falasdinawa
Tana jaddada cewa: Muggan makaman gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila suna ci gaba da lakume rayukan fararen hula a zirin Gaza. Sannan a wani sabon kisan kiyashi, an kashe Falasdinawa 7 a wani harin da sojojin mamayar Isra’ila suka kai kan wani gida a Jabaliya da ke arewacin zirin Gaza.
A wani kisan kiyashi kuma jami’an tsaron farar hula a Gaza sun sanar da mutuwar yara tara da suka kone kurmus a wani harin da sojoji mamayar Isra’ila suka kai kan Khan Yunis da ke kudancin zirin Gaza da aka killace. An kuma kashe wani Bafalasdine tare da raunata wasu a wani harin da aka kai kan wata tanti da ke dauke da ‘yan gudun hijira a yankin Al-Mawasi da ke yammacin Khan Yunis.
A wani bangare na yakin yunwa, ma’aikatar lafiya a Gaza ta sanar da mutuwar wani yaro sakamakon yunwa da kuma killace yankin da aka yi domin hana aikewa da kayan agajin jin kai. A baya dai ma’aikatar lafiyar ta Gaza ta bayyana cewa: Yara da tsofaffi 29 ne suka mutu sakamakon matsalar yunwa, sannan kuma wasu dubbai na cikin hadarin mutuwa ta dalilin haka.
Hukumar samar da abinci ta duniya ta tabbatar da cewa dubun dubatar yara na fuskantar matsanancin rashin abinci mai gina jiki. Wani jami’in Majalisar Dinkin Duniya ya kuma yi gargadin cewa jarirai 14,000 na iya mutuwa ba tare da shigar da agaji yankin ba.