Daga Bello Wakili

Mataimaki na Musamman ga Shugaban Kasa kan Harkokin Yada Labarai da Ayyuka na Musamman, Mista Tunde Rahman, ya bayyana jerin goyon bayan da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ke samu daga cikin jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a matsayin shaida mai karfi kan tsare-tsaren da gwamnati ta aiwatar cikin shekaru biyu da suka gabata.

A yayin wata tattaunawa da ya yi da Radio Nigeria a Abuja, Mista Rahman ya ce goyon bayan da ke fitowa daga gwamnoni na APC, ‘yan majalisar dokoki da shugabannin jam’iyya, na nuna karuwar amincewa da sauye-sauyen tattalin arzikin da Shugaba Tinubu ya aiwatar. Ya ce wannan ya hada da cire tallafin fetur da daidaita farashin canjin kudade.

“Wadannan goyon bayan suna da matukar muhimmanci. Su ne jinjina ga jarumtaka da kwarin gwiwar Shugaban kasa, musamman wajen daukar matakai masu wahala tun farkon wa’adinsa, kamar cire tallafin man fetur a ranar 29 ga Mayu, 2023,” in ji shi.

A cewarsa, tasirin wadannan matakai ya fara haifar da sakamako mai kyau, ciki har da farfadowar tattalin arziki, saukin darajar Naira da kuma dan saukin farashin kayan abinci.

Ya kara da cewa shugabannin jam’iyya da mambobinta sun fahimci amfanin wadannan tsare-tsare, shi ya sa suke marawa Shugaban kasa baya.

Da aka tambaye shi ko wannan amincewar baiyi wuri ba alhali sauran kusan shekaru biyu kafin zabe, Mista Rahman ya ce hakan ba sabon abu ba ne a siyasar Najeriya, domin har jam’iyyun adawa sun riga sun fara shirin tunkarar zabe.

“Baiyi wuri ba. APC na mayar da martani ne ga abubuwan da ke faruwa a siyasa. Abin da ke faruwa yanzu wani nau’in tantancewa ce ta wa’adin gwamnati,” in ji shi.

Mista Rahman ya kuma ambaci sauya shekar gwamnan Jihar Delta zuwa APC tare da wasu daga cikin mambobin majalisar dokoki da masu rike da mukamai a gwamnatinsa a matsayin karin hujjar karuwar goyon bayan da Shugaba Tinubu ke samu.

Ya kammala da cewa a yi tsammanin karin goyon baya da sauya sheka daga gun wainda ba yan jamiyar APC ba nan gaba kadan yayin da gwamnatin ke ci gaba da nuna nasara da kwanciyar hankali a kasar.

BELLO WAKILI 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Goyon Bayan Takara goyon bayan da

এছাড়াও পড়ুন:

An ceto mutum 6 daga hannun masu garkuwa a Kebbi

Wata rundunar haɗin gwiwa ta jami’an tsaro ta samu nasarar kuɓutar da wasu mutane shida da aka yi garkuwa da su da shanu da aka sace a Jihar Kebbi.

Bayanai sun ce an sace mutanen da dabbobin ne a ƙauyukan Ukuhu da Kokanawa a Karamar Hukumar Danko Wasagu ta jihar.

‘ADC za ta mayar da APC jam’iyyar adawa a 2027’ Gwamnatin Tinubu na shirya mana zagon ƙasa — ADC

Wani daraktan tsaro a Gwamnatin Kebbi, Abdurrahama Zagga ne ya sanar wa manema labarai nasarar da aka samu a ranar Talata, inda ya ce an kai samamen ne bayan umarni da aka samu daga Gwamna Nasiru Idris bisa bayanan sirri da aka tattaro a yankin.

A cewar Zagga, tawagar jami’an tsaro ta fatattaki ’yan ta’addan da suka yi garkuwa da mutanen da kuma shanun da suka sace a wani gulbi da ke iyaka da Jihar Zamfara.

“Mutane da aka ceto an mika su ga iyalansu. Kuma wannan abin farin ciki ne ga gwamna musamman a kokarin da jami’an tsaro suke yi, lamarin da zai kara inganta zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin masarautar Zuru.”

Ya bayyana fatan da suke da shi na kawar da ɓarayin shanu da ’yan bindigar Lukurawa a yankin Zuru da Argungu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sauye-sauyen Tinubu Suna Taimaka Wa Farfaɗowar Tattalin Arzikin Nijeriya — Minista
  • Tinubu ne ya buɗe wa Buhari ƙofar zama shugaban ƙasa — Hadimi
  • Ba Tinubu kaɗai ne ya sa Buhari ya ci zaɓe a 2015 ba – Boss Mustapha
  • Tinubu Bai Taɓa Ba Ni Umarnin Yin Ƙarya Ko Cin Zarafin ’Yan Jarida Ba – Minista
  • 2027: Idan ADC na son lashe zaɓe dole ta bai wa ɗan Arewa takara — Okonkwo
  • Kazem Sajjadpour Ya ce: Iraniyawa Suna Daukan Tarayyar Turai Ma Goyon Bayan Harin Zaluncin Isra’ila Kansu
  • Har Yanzu Ba A Ga Mutum 160 Bayan Ambaliyar Texas
  • Kofin Duniya: Chelsea Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Ta Doke Fluminense
  • DAGA LARABA: Shin Ko Zafin Nema Na Kawo Samu?
  • An ceto mutum 6 daga hannun masu garkuwa a Kebbi