Daga Bello Wakili

Mataimaki na Musamman ga Shugaban Kasa kan Harkokin Yada Labarai da Ayyuka na Musamman, Mista Tunde Rahman, ya bayyana jerin goyon bayan da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ke samu daga cikin jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a matsayin shaida mai karfi kan tsare-tsaren da gwamnati ta aiwatar cikin shekaru biyu da suka gabata.

A yayin wata tattaunawa da ya yi da Radio Nigeria a Abuja, Mista Rahman ya ce goyon bayan da ke fitowa daga gwamnoni na APC, ‘yan majalisar dokoki da shugabannin jam’iyya, na nuna karuwar amincewa da sauye-sauyen tattalin arzikin da Shugaba Tinubu ya aiwatar. Ya ce wannan ya hada da cire tallafin fetur da daidaita farashin canjin kudade.

“Wadannan goyon bayan suna da matukar muhimmanci. Su ne jinjina ga jarumtaka da kwarin gwiwar Shugaban kasa, musamman wajen daukar matakai masu wahala tun farkon wa’adinsa, kamar cire tallafin man fetur a ranar 29 ga Mayu, 2023,” in ji shi.

A cewarsa, tasirin wadannan matakai ya fara haifar da sakamako mai kyau, ciki har da farfadowar tattalin arziki, saukin darajar Naira da kuma dan saukin farashin kayan abinci.

Ya kara da cewa shugabannin jam’iyya da mambobinta sun fahimci amfanin wadannan tsare-tsare, shi ya sa suke marawa Shugaban kasa baya.

Da aka tambaye shi ko wannan amincewar baiyi wuri ba alhali sauran kusan shekaru biyu kafin zabe, Mista Rahman ya ce hakan ba sabon abu ba ne a siyasar Najeriya, domin har jam’iyyun adawa sun riga sun fara shirin tunkarar zabe.

“Baiyi wuri ba. APC na mayar da martani ne ga abubuwan da ke faruwa a siyasa. Abin da ke faruwa yanzu wani nau’in tantancewa ce ta wa’adin gwamnati,” in ji shi.

Mista Rahman ya kuma ambaci sauya shekar gwamnan Jihar Delta zuwa APC tare da wasu daga cikin mambobin majalisar dokoki da masu rike da mukamai a gwamnatinsa a matsayin karin hujjar karuwar goyon bayan da Shugaba Tinubu ke samu.

Ya kammala da cewa a yi tsammanin karin goyon baya da sauya sheka daga gun wainda ba yan jamiyar APC ba nan gaba kadan yayin da gwamnatin ke ci gaba da nuna nasara da kwanciyar hankali a kasar.

BELLO WAKILI 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Goyon Bayan Takara goyon bayan da

এছাড়াও পড়ুন:

Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori

Bug da kari Tinubu ya jinjina wa Shugaban jami’ar, Farfesa Wahab Olasupo Egbewole (SAN)da ‘yan tawagarsa wajen maida hankalin da suka yi na bunkasa Jami’ar da kumna kudurinta na muradun ci gaban da ake bukata.

Shi ma anashi jawabin Shugaban Jami’ar Sarkin Katsina, Alhaji. Abdulmumin Kabir Usman, wanda Wazirin Katsina, Sanata Ibrahim Idah ya wakilta, ya nuna jin dadinsa kan irin kokarin da UNILORIN saboda bunkasar ilimi da kumasamar wuraren koyon kaaratu masu kyau da kuma suka dace.

Ya yi ma kallon ayyukan da ak kaddamar a matsayin“ irin abubuwan da ake bukatar gani ke nan”da za su taimakawa lamarin koyarwa, koyo,da kuma bincike, inda ya kara da cewa yadda Jami’ar ta maida hankalinta wajen bunkasa dabarar koyon yin abubuwa zai taimakawa dalibai su tashi da sun koyi abubuwan da zasu yi baya rayuwar da suka yi cikin aji.

A nashi jawabin mataimakin Shugaban Jami’ar, Farfesa. Egbewole ya nuna farin cikinsa da godew a Shugaban kasa Tinubu kan yadda ya amince da gaiyar da Jami’ar ta yi ma shi, da kuma taimaka mata wajen tafiyar da bunkasar abubuwan jin dadi.

“Muna nan muna sa ido saboda ci gaban samun abubwan da suke taimakawa ci gaba kwarai da gaske a kowace rana kamar yadda yace yana da amincewa da yardarm ci gaba da samun hakan’’.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna November 1, 2025 Manyan Labarai Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami November 1, 2025 Manyan Labarai Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 20, Sun Ceto Mutane 17 Da Aka Yi Garkuwa Da Su November 1, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori
  • Kwamitin Tsaron MDD ya goyi bayan shirin Morocco game da yankin Yammacin Sahara
  • An Tube Yarima Mai Jiran Gado Na Birtaniya Bayan Da Aka Tabbatar Da Laifinsa
  • Zaben 2027 Zai Kasance Ne Tsakanin Mulkin Tinubu Da Zabin Ƴan Nijeriya —Atiku Abubakar
  • NAJERIYA A YAU: Dalilan Da Daliban Makarantar Kudi Suka Fi Na Gwamnati Kokari
  • Ci Gaba Da Killace Gaza Bayan Tsagaita Bude Wuta Ya Janyo Mutuwar Mutane 1000 A Yankin
  • Tinubu Ya Amince Da Ƙara Harajin Shigo Da Man Fetur Da Dizal Zuwa Kashi 15
  • Matashi ya rasa ransa a kan soyayya a Yobe
  • Bai Kamata Gwamnati Ta Ke Ciyo Bashi Bayan Cire Tallafin Man Fetur Ba – Sanusi II
  • Bai Kamata Gwamnati Ta Ke Ciyo Bashi Bayan Cire Tallafin Man Fetur – Sanusi II