An Gudanar Da Dandalin Kawancen Birane Na Kasa Da Kasa Na Shanghai
Published: 30th, May 2025 GMT
A yau Alhamis ne aka gudanar da dandalin “Kasa da kasa na tattaunawa tsakanin magadan biranen duniya na Shanghai, da dandalin kawancen birane na kasa da kasa na Shanghai na shekarar 2025.”
Magadan birane da wakilai daga birane 26 dake cikin kawancen, daga sassan kasashen duniya 22, sun hallara a bakin kogin Huangpu, domin tattaunawa, da musaya game da yanayin makomar birane a nan gaba, da hadin gwiwa, inda suka mayar da hankali kan “Bunkasa birane masu korayen itatuwa, da karancin fitar da iskar carbon, da ci gaba da kirkire-kirkire”.
Kazalika a yau din, birnin Shanghai ya sanya hannu kan takardun bunkasa kawance da musaya tare da Tbilisi na Georgia, da Vientiane na Laos da sauransu. A shekarun baya bayan nan, biranen kasa da kasa dake shiga kawance da birnin Shanghai na ta karuwa. Inda ya zuwa yanzu, birnin ya gina kawance tare da birane 95 na kasashe 59 dake fadin duniya. (Mai fassara: Saminu Alhassan)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Gombe ta rattaba hannu kan kwangilar biliyan 48 na aikin zaizayar Kasa
Jihar Gombe ta rattaba hannu kan kwangilar sama da biliyan 48 don aikin kula da Makarantar ‘yan mata ta Mega dake Doma da kuma zaizayar kasa
Baya ga sanya hannu kan kwangilar, an kuma bayar da cak don biyan diyya ga mazauna yankin mai nisan mita 10 da ke kan hanyar aikin.
Da yake jawabi a wurin rattaba hannu kan kwangilar a hukumance a Hayin Missau Bogo, Gwamna Inuwa Yahaya ya bayyana matakin a matsayin wani muhimmin mataki na tabbatar da muhallin Gombe da kuma kare makomar jama’a.
A cewarsa aikin ba wai kawai zai shawo kan zaizayar kasa ba ne zai dawo da fata ga al’ummomin da abin ya shafa.
Alh. Inuwa Yahaya wanda ya bada umarnin kammala aikin a cikin watanni 30 ya bukaci dan kwangilar da ya gabatar da aiki mai inganci.
Ya yi kira ga sarakunan gargajiya da shugabannin al’umma da su ci gaba da taka muhimmiyar rawa wajen wanzar da zaman lafiya da juna a tsakanin al’umma, da kuma kiyaye ayyukan da ba su dace ba kamar sare itatuwa da zubar da shara da ke cutar da muhalli.
Shima da yake jawabi kwamishinan albarkatun ruwa da muhalli da gandun daji na jihar Gombe Mal. Muhammad Fawu, ya yabawa hadin gwiwar da gwamnatin Gombe da Bankin Duniya suka yi wajen samar da kudaden aikin, ya ce wani gagarumin kokari ne na kare muhalli da kuma tabbatar da makomar al’umma.
KARSHEN HUDU