Aminiya:
2025-05-27@19:23:32 GMT

Wani abu ya fashe kusa da barikin soji a Abuja

Published: 27th, May 2025 GMT

Rundunar ‘yan sandan Birnin Tarayya ta buƙaci al’ummar da ke kewayen hanyar Mararaba zuwa Nyanya su kwantar da hankalinsu bayan jin ƙarar wani abu da ya fashe a yammacin ranar Litinin.

Lamarin ya faru ne a wata tashar bas da ke kusa da barikin sojoji na Mogadishu a kan hanyar Mararaba zuwa Nyanya.

A wata sanarwa da rundunar ta fitar mai ɗauke da sa hannun kakakinta, Josephine Adeh, ta ce tuni ta tura jami’anta wajen domin bincike da kuma tabbatar da zaman lafiya a yankin.

Kwastam ta kama Tiramol ta N150m, ta miƙa wa NAFDAC a Kano FCTA ta rufe hedikwatar PDP saboda rashin biyan haraji

“A ranar 26 ga watan Mayu da misalin ƙarfe 2:15 na rana aka yi mana kiran gaggawa kan wani abu ya fashe a shatale-shatalen hanyar Mararaba-Nyanya.

“Muna samun rahoton jami’anmu da ke sashen da abun ya shafa suka dira a wajen in da suka kange wurin.

“Mun samu nasarar ceto mutum guda da ya samu rauni, kuma yana asibiti yana karɓar magani.

“Muna nan muna bincike domin gano abin da ya fashe, da kuma musabbabin hakan.

Daga nan ne rundunar ta bukaci al’ummar yankin su ci gaba da harkokinsu ba tare da wata fargaba ba, su kuma miƙa wa rundunar duk wani motsi da ba su amince da shi ba.

Rahotanni sun bayyana cewa wanda ya tayar da bam ɗin ya mutu.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Birnin tarayya Tsaro

এছাড়াও পড়ুন:

Ana zargin wani mutum da kashe ɗan maƙwabtansa a Sakkwato

An shiga ruɗani a unguwar CBN Quarters da ke cikin birnin Sakkwato, inda wani ƙaramin yaro ɗan shekara huɗu mai suna Ayman Abubakar, ya ɓace, amma daga bisani aka gano gawarsa a cikin ramin sokawe.

Ana zargin wani maƙwabcin iyayen yaron da wata mata da aikata wannan ɗanyen aiki.

An kashe matashi yayin rikici a ƙauyukan Kano Gwamnatin Gombe za ta taimaki ’yar shekara 14 da aka yi wa auren dole

Ƙngiyoyi da ke fafutukar kare haƙƙin yara da martabar bil adama sun bayyana wannan kisa a matsayin babban cin zarafi.

A cikin wata sanarwar haɗin gwiwa da suka fitar, shugaban NACTAL na ƙasa Abdulganiyu Abubakar, Usman Ahmad daga ƙungiyar kare haƙƙin yara, da Rabi’u Bello Gandi shugaban hukumar kare cin zarafin jinsi, sun yi Allah-wadai da kisan yaron.

“Kashe wannan ƙaramin yaro cin zarafi ne na keta haƙƙin ɗan Adam, kuma lamarin da ya saɓa da doka.

“Wannan mummunan abu ne da ke ƙara nuna irin haɗuran da yara ke fuskanta a cikin al’umma.”

Ƙungiyoyin sun buƙaci a gudanar da bincike don gano gaskiya tare da ɗaukar matakin hukunta duk wanda ke da hannu a kisan.

“Muna kira da a tabbatar da an yi gaskiya da adalci, a kuma hukunta waɗanda ke da hannu a kisan Ayman. Hakazalika, ya zama dole a riƙa bayyana wa jama’a irin ci gaban da ake samu a yayin bincike lokaci bayan lokaci.”

Sun jaddada buƙatar a ɗauki matakan gaggawa na kare yara daga faɗa wa hannun miyagu.

“Kare haƙƙin yaron ɗan Najeriya lamari ne da ya kamata a bai wa fifiko a ƙasa, a daina wasa da shi.”

Mahaifin Ayman, Dakta Abubakar, ya bayyana damuwarsa kan yadda lamarin ya faru.

“Na rasa ɗana ne ranar 29 ga watan Maris, bayan ya dawo daga sallar La’asar. Mun yi ta nemansa har tsawon sati bakwai ba tare da nasara ba. Daga baya sai aka gano gawarsa a cikin ramin sokawe.”

Ya roƙi al’umma su mara masa baya wajen ganin an yi wa ɗansa adalci.

Rundunar ’yan sandan jihar, tabbatar da cewa ta kama waɗanda ake zargi, kuma an fara gudanar da bincike a kansu.

Ƙungiyoyin sun yi alƙawarin ganin cewa sun bibiyu lamarin don tabbatar da gaskiya da adalci.

“Za mu tsaya tare da iyayen Ayman domin tabbatar da cewa an yi adalci. Adalci ga Ayman, adalci ne ga kowa.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Raya Al’adu Wani Sirri Ne Na Ci Gaban Kasar Sin
  • Sojojin Yahudawa sun Kashe Wani Matashi A Yankin Yamma Da Kogin  Jordan
  • ‘Yansanda Sun Nemi A Kwantar Da Hankula Bayan Fashewar Wani Abu A Abuja
  • Falasdinawa 30 sun yi shahada a Wani harin Isra’ila kan wata makaranta
  • Sojojin Yamen Sun Cilla Wani Makamai Masu Linzami Kan HKI
  • Sheikh Na’im Kassim: Gwagwarmaya Tana Da Wata Hanyar Ta Korar ‘Yan Mamaya
  • Ana zargin wani mutum da kashe ɗan maƙwabtansa a Sakkwato
  • ‘Yar Majalisar Dokokin Ireland Ta Yi Suka Kan Shugabannin Turai Tare Da Neman Afuwa Daga Falasdinawa
  • An kashe matashi yayin rikici a ƙauyukan Kano