Wani abu ya fashe kusa da barikin soji a Abuja
Published: 27th, May 2025 GMT
Rundunar ‘yan sandan Birnin Tarayya ta buƙaci al’ummar da ke kewayen hanyar Mararaba zuwa Nyanya su kwantar da hankalinsu bayan jin ƙarar wani abu da ya fashe a yammacin ranar Litinin.
Lamarin ya faru ne a wata tashar bas da ke kusa da barikin sojoji na Mogadishu a kan hanyar Mararaba zuwa Nyanya.
A wata sanarwa da rundunar ta fitar mai ɗauke da sa hannun kakakinta, Josephine Adeh, ta ce tuni ta tura jami’anta wajen domin bincike da kuma tabbatar da zaman lafiya a yankin.
“A ranar 26 ga watan Mayu da misalin ƙarfe 2:15 na rana aka yi mana kiran gaggawa kan wani abu ya fashe a shatale-shatalen hanyar Mararaba-Nyanya.
“Muna samun rahoton jami’anmu da ke sashen da abun ya shafa suka dira a wajen in da suka kange wurin.
“Mun samu nasarar ceto mutum guda da ya samu rauni, kuma yana asibiti yana karɓar magani.
“Muna nan muna bincike domin gano abin da ya fashe, da kuma musabbabin hakan.
Daga nan ne rundunar ta bukaci al’ummar yankin su ci gaba da harkokinsu ba tare da wata fargaba ba, su kuma miƙa wa rundunar duk wani motsi da ba su amince da shi ba.
Rahotanni sun bayyana cewa wanda ya tayar da bam ɗin ya mutu.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Birnin tarayya Tsaro
এছাড়াও পড়ুন:
Masu ƙwacen waya sun kashe ma’aikaciyar ofishin jakadancin Ghana a Abuja
Masu kwacen da aka fi san da ’yan ‘One Chance’, sun kashe Freda Arnong, wata ma’aikaciya a ofishin jakadancin kasar Ghana da ke babban birnin tarayya Abuja.
Bayanai sun nuna matar, wacce daga bisani ta mutu a asibitin kasa da ke Abuja, ta hau motar da ake zargin ta masu kwacen ce a bisa rashin sani.
Wata majiya daga jami’an tsaro ta shaida wa wakilinmu cewa Freda ta hau motar ta tasi ne daga marabar otal din Transcorp a makon da ya gabata.
Kaso 90 na ’yan bindigar da suka addabi Katsina ’yan asalin jihar ne – Radda ‘Abin da zai sa APC ba za ta taɓa mantawa da Ganduje ba’Majiyar ta ce a lokacin da matar ta shiga, akwai wasu mutum hudu da har yanzu ba a kai ga tantance su ba.
Majiyar ta ce daga nan ne sai direban motar ya canza hanya ya bi titin zuwa Lugbe-filin jirgin sama, inda suka kashe ta, kafin daga bisani su jefar da gawarta yayin da motar ke ci gaba da tafiya.
Daga nan ne aka dauke ta aka garzaya da ita asibitin, inda daga bisani ta rasu a ranar Talata.
Ita ma wata majiya daga asibitin da ta ce ba ta da hurumin yin magana da ’yan jarida ta tabbatar da mutuwar matar.
“Ta mutu wajen misalin karfe 1:52 na ranar Talata, kuma yanzu haka gawarta tana dakin adana gawarwaki na asibitin domin yin binciken musabbabin mutuwar tata,” in ji majiyar.
Sai dai da wakilinmu ya tuntubi Kakakin rundunar ’yan sanda ta yankin Abuja, SP Adeh Josephine, amma ba ta amsa kira ko sakon kar-ta-kwanan da ya tura mata ba, har zuwa lokacin hada wannan rahoton.