HausaTv:
2025-09-18@00:56:27 GMT

Shugaban  Iran na ziyarar aiki a kasar Oman

Published: 28th, May 2025 GMT

Shugaban kasar Iran, Massoud Pezeshkian, ya fara wata ziyarar aiki a kasar Oman mai manufar karfafa dangantaka tsakanin kasashen biyu aminnan juna.

Shugaba Pezeshkian ya yaba da rawar da Oman ta taka a tattaunawar dake tsakanin Iran da Amurka, kuma tana fatan za a cimma sakamako mai kyau.

Pezeshkian ya bayyana hakan ne yayin ganawa da ya yi da Sultan Haitham bin Tariq na Oman a birnin Muscat a yammacin yau Talata.

Da yake jaddada matsayin kasar Oman a cikin manufofin ketare na Iran, Pezeshkian ya ce Tehran na da cikakkiyar amincewa ga Oman, kuma wannan amana na karfafa alaka tsakanin kasashen biyu.

Shugaban ya ce Iran a shirye ta ke ta inganta hadin gwiwa da Oman a dukkan fannoni, yana mai imani cewa kasashen biyu suna da karfin da za a iya amfani da su don cin moriyar juna da sauran al’ummomin yankin,” in ji shi.

Ya ce Iran a shirye take ta inganta hadin gwiwa da Oman a fannonin, kimiyya, ilimi, da fasaha, musamman a fannin likitanci.

A nasa bangare Sultan Haitham ya bayyana cewa ya yarda idan aka bude hanyoyin gudanar da harkokin kasuwanci, kasashen biyu za su samu gagarumin ci gaba a huldar dake tsakaninsu.

Dangane da tattaunawar dake tsakanin Iran da Amurka, Sultan Haitham ya ce Muscat ta shiga tsakani a tattaunawar da alheri,” in ji shi.

Sarkin na Oman ya kuma yaba da matsayin Iran na kare al’ummar Falasdinu.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Larijani: Iran Da Saudiyya Za Su Bunkasa Aiki Tare A Fagagen Kasuwanci Da Tsaro
  • Gwamnatin Kano Ta Inganta Cibiyoyin Horas Da Sana’o’i Domin Dakile Aikata Laifuka Tsakanin Matasa
  • Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok
  • Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi
  • Pezeshkian: Saudiyya Na Iya Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Samar Da Hadin Kan Kasashen Musulmi
  • Pezeshkian: Ta’addancin Haramtacciyar Kasar Isra’ila Kan Kasar Qatar Zalunci Ne Ga Diflomasiyya
  • Pezeshkian: Ya kamata kasashen musulmi su yanke alaka da gwamnatin sahyoniya tare da kiyaye hadin kai
  • Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne
  • Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu
  • Shugaban Kasar Iran Ya Gana Da Sarkin Kasar Qatar A Birnin Doha