Shugaban Iran na ziyarar aiki a kasar Oman
Published: 28th, May 2025 GMT
Shugaban kasar Iran, Massoud Pezeshkian, ya fara wata ziyarar aiki a kasar Oman mai manufar karfafa dangantaka tsakanin kasashen biyu aminnan juna.
Shugaba Pezeshkian ya yaba da rawar da Oman ta taka a tattaunawar dake tsakanin Iran da Amurka, kuma tana fatan za a cimma sakamako mai kyau.
Pezeshkian ya bayyana hakan ne yayin ganawa da ya yi da Sultan Haitham bin Tariq na Oman a birnin Muscat a yammacin yau Talata.
Da yake jaddada matsayin kasar Oman a cikin manufofin ketare na Iran, Pezeshkian ya ce Tehran na da cikakkiyar amincewa ga Oman, kuma wannan amana na karfafa alaka tsakanin kasashen biyu.
Shugaban ya ce Iran a shirye ta ke ta inganta hadin gwiwa da Oman a dukkan fannoni, yana mai imani cewa kasashen biyu suna da karfin da za a iya amfani da su don cin moriyar juna da sauran al’ummomin yankin,” in ji shi.
Ya ce Iran a shirye take ta inganta hadin gwiwa da Oman a fannonin, kimiyya, ilimi, da fasaha, musamman a fannin likitanci.
A nasa bangare Sultan Haitham ya bayyana cewa ya yarda idan aka bude hanyoyin gudanar da harkokin kasuwanci, kasashen biyu za su samu gagarumin ci gaba a huldar dake tsakaninsu.
Dangane da tattaunawar dake tsakanin Iran da Amurka, Sultan Haitham ya ce Muscat ta shiga tsakani a tattaunawar da alheri,” in ji shi.
Sarkin na Oman ya kuma yaba da matsayin Iran na kare al’ummar Falasdinu.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Jagoran Juyin Juya Halin Musulunci Ya Ce: Dole Ne A Dauki Kwararan Matakan Don Dakatar Da Laifukan Gaza
Jagoran juyin juya halin Musulunci ya jaddada cewa: Dole ne a dauki kwararan matakai don dakatar da laifukan da ake yi a Gaza
A yayin ganawarsa da fira ministan Pakistan Shehbaz Sharif da tawagarsa a yammacin yau, Jagoran juyin juya halin Musulunci Ayatullah Sayyid Ali Khamenei ya jaddada wajabcin gudanar da ayyukan hadin gwiwa da inganci tsakanin kasashen Iran da Pakistan domin dakile laifukan da yahudawan sahayoniyya suke aikatawa a Gaza.
A farkon taron, Jagoran juyin juya halin Musulunci ya bayyana matsayin Pakistan na musamman a duniyar Musulunci, inda ya bayyana jin dadinsa da kawo karshen yakin da ake yi tsakanin Pakistan da Indiya, tare da bayyana fatansa na warware sabanin da ke tsakanin kasashen biyu ta hanyar lumana.
Haka nan kuma ya yi ishara da matsayar da Pakistan ta dauka kan batun Falastinu a cikin wadannan shekaru da suka gabata, yana mai cewa: Duk da cewa a cikin ‘yan shekarun nan a kodayaushe ana fuskantar kalubale ga kasashen musulmi na kulla alaka da yahudawan sahayoniyya, Pakistan ba ta taba samun irin wadannan fitintinu ba.