Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu ya amince da ɗaga darajar Kwalejin Kimiyya da Kere-kere ta Tarayya da ke Kabo a jihar Kano, zuwa Jami’ar Kimiyya da Fasaha ta Tarayya, Kabo.

Wannan cibiyar ilimi, wacce aka kafa a shekarar 2022, yanzu ta zama jami’a ta uku ta gwamnatin tarayya a jihar, bayan Jami’ar Bayero Kano da kuma Jami’ar Ilimi ta Tarayya da aka assasa a  kwanan nan, wacce aka sanya wa sunan marigayi Yusuf Maitama Sule.

Matashi ya shiga hannun ’yan sanda kan kisan matar aure a Kano Tinubu zai ciyo bashin Naira tiriliyan 39 daga kasashen waje

Kano na kuma da jami’o’o’i biyu mallakin gwamnatin jiha.

Wannan ci gaban ya zo ne a daidai lokacin da ake fama da damuwa game da samar da kuɗaɗe ga manyan cibiyoyin da makarantu na gwamnati da kuma yawaitar sabbin da ake kafawa.

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau I. Jibrin, wanda ya gabatar da ƙudirin dokar, ya yaba wa Shugaba Tinubu bisa amincewa da ƙudirin.

A yayin zaman Majalisar Dattawa na ranar Talata, an karanta wasiƙun shugaban kasa game da kafa sabbin jami’o’i a jihohin Kano, Akwa Ibom, da Oyo.

Sanata Barau, a cikin wata sanarwa da mai taimaka masa kan harkokin yada labarai, Ismail Mudashir, ya bayar, ya ce sauya fasalin ya yi daidai da kyawawan halaye na duniya a fannin ilimi kuma yana da nufin inganta samun damar yin manyan makarantu.

Ya ce: “Kafa Jami’ar Kimiyya da Kere-kere ta Tarayya ta Kabo, yana nuna jajircewar Shugaban ƙasa wajen bai wa matasan Najeriya muhimman dabarun samun ƙwarewa a fannoni irin su kere-kere da basirar na’ura da fasahar sarrafa na’ura mai kwakwalwa, da kuma an fasahar tsaron intanet.”

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Barau

এছাড়াও পড়ুন:

 Yemen: Wuce Gona Da Irin HKI Ba Zai Sauya Mana Ra’ayi Akan Ci Gaba Da Taimaka Wa Gaza Ba

Shugaban kungiyar Ansarullah ta kasar Yemen Sayyid Abdulmalik al-Husi ya bayyana cewa; Harin da “Isra’ila” ta kai wa filin saukar jiragen saman Sanaa, manufarsa  ita ce yin matsin lamba akan matsayarmu ta taimakawa al’ummar Falasdinu da ake zalunta.”

Sayyid Abdulmalik al-Husi ya kara da cewa;  Komai girman hare-haren da Isra’ilan za ta kai ba zai yi tasiri akan matsayarmu ta taimakawa Gaza ba,sannan kuma ya kara da cewa; Abinda Isra’ila makiya ke son yi, shi ne a kyale ta yi yadda take so da Falasdinawa ba tare da an mayar mata da martani ba daga kowace kasa ta musulmi.”

Shugaban kungiyar ta Ansarullah ya kuma ce; Matsayar da kasar Yemen take dauka na taimakawa Falasdinawa, matsaya ce ta addini.”

Haka nan kuma ya kara da cewa; Daga cikin manufofin harin na Isra’ila a filin saukar jiragen sama na Sanaa da akwai dakatar da jigilar mahajjata, amma ba za su yi nasara ba.”

Shugaban kungiyar ta Ansarullah ya yi ishara da wahalhalun da al’ummar Gaza suke ciki,sannan kuma ya ce; A wannan lokacin wahalhalun na mutanen Falasdinu sun fi na baya, domin suna fuskantar yunwa da kuma ci gaba da kai hare-hare da Isra’ila take yi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  •  Yemen: Wuce Gona Da Irin HKI Ba Zai Sauya Mana Ra’ayi Akan Ci Gaba Da Taimaka Wa Gaza Ba
  •  Kasar Chile Na Shirin Yanke Alakar Diplomasiyya Da “Isra’ila”
  • Birtaniya ta dage takunkumin da ta kakaba wa wasu manyan jami’an Zimbabwe
  • Shugaban Kasar Iran Ya Kai Ziyara Zuwa Kasar Oman don Karfafa Kyakkyawar Alakar Kasashen Biyu
  • Shugaba Tinubu Ya Amince Da Ɗaga Likafar Kwalejin Fasaha Ta Kabo Zuwa Jami’a
  • Shugaba Tinubu Ya Amince Da Sauya Kabo Polytechnic Zuwa Jami’ar Kimiyya Da Fasaha Kabo
  • Rundunar Ƴansanda Ta Gayyaci Jami’anta Da Bidiyonu Ya Yaɗu Suna Karɓar Cin Hancin Naira 5000
  • Xi Ya Taya Jami’ar Fudan Murnar Cika Shekaru 120 Da Kafuwa
  • Babu Wasu Masu Juya Tinubu Ta Bayan Fage Ministan Yaɗa Labarai