A cikin wani mataki na ci gaba da sauya fasalin bangarorin noma da kiwo, Gwamnatin Jihar Jigawa na shirin kulla yarjejeniyar hadin gwiwa da daya daga cikin manyan kamfanonin kiwon kaji na kasar Indiya, wato Srinivasa Farms.

Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan jihar Jigawa, Hamisu Mohammed Gumel, ya fitar.

Ya ce a wani bangare na ziyarar zuba jari a fannin noma da gwamnatin jihar ke gudanarwa zuwa kasar Indiya, tawagar jihar karkashin jagorancin Gwamna Malam Umar Namadi ta kai ziyara ofishin babban kamfanin Srinivasa Farms dake birnin Hyderabad domin tattauna damar hadin gwiwa da nufin farfado da harkar kiwon kaji a Jigawa.

Hamisu Mohammed Gumel ya kara da cewa ana sa ran za a rattaba hannu kan wata takardar yarjejeniyar fahimtar juna (MoU) a makonni masu zuwa domin kulla wannan hadin gwiwa, wanda zai bude kofa ga musayar ilimi, zuba jari daga masu zaman kansu, da ci gaba mai dorewa a bangaren kiwon kaji na jihar Jigawa.

Yayin da yake jawabi a lokacin ziyarar, Gwamna Namadi ya bayyana kwarin gwiwarsa kan tasirin wannan shiri.

Ya ce hadin gwiwar wani babban ci gaba ne wajen cika alkawurransa na sauya fasalin harkar noma, inda ya kara da cewa da fasaha ta zamani, horo, da hadin gwiwa irin wannan, Jigawa za ta zama cibiyar kiwon kaji ta kwarai a Najeriya.

Ziyarar tawagar zuwa kasar Indiya na daga cikin wani yunkuri na kasa da kasa wajen samar da hadin gwiwa, gogewa da kirkire-kirkire da suka yi daidai da Manufar Makomar Ci Gaban Tattalin Arziki da Samun Isasshen Abinci ta Matakai 12 da Jihar Jigawa ta tsara.

 

Usman Mohammed Zaria

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Indiya Jigawa jihar Jigawa hadin gwiwa

এছাড়াও পড়ুন:

Akwai Ma’ana Mai Zurfi A Bayan Da’a

 

Tabbas a halin yanzu, wasu kasashe ba su ba da’a muhimmanci ba, kana suna ta daukar matakan kashin kai yadda suka ga dama, lamarin da ya sa al’amuran kasa da kasa suka shiga rudani. Dangane da wannan batu, dole ne Sin da kasashen Afirka masu da’a su karfafa hadin kai, su yi adawa da siyasar nuna fin karfi, da daukaka ra’ayin cudanyar mabambantan bangarori masu fada-a-ji a duniya, da kare tsarin kasa da kasa dake karkashin jagorancin Majalisar Dinkin Duniya. Ta la’akari da yadda adadin yawan al’ummar Sin da Afirka ya kai kashi daya bisa uku na yawan al’ummar duniya, kokarin hadin gwiwarmu tabbas zai karkata duniya zuwa ga turba mai dacewa. (Bello Wang)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Majalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince Da Dokokin Ilimin Noma da Gyaran Kotunan Gargajiya
  • Sanarwar Bayan Taron Kolin Sin Da ASEAN Da GCC Ta Yi Nuni Ga Burin Kara Dunkulewa Waje Guda
  • Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Ayukka 16 A Sakkwato
  • Hadin Gwiwar Sin Da Yankin Turai Na Kara Kawo Haske Ga Tattalin Arzikin Duniya
  • An Fitar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Ta Taron Kolin ASEAN-Sin-GCC
  • Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Nuna Misali Na Bude Kofa Da Raya Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da ASEAN Da GCC
  • Raya Al’adu Wani Sirri Ne Na Ci Gaban Kasar Sin
  • Akwai Ma’ana Mai Zurfi A Bayan Da’a
  • Gwamnatin Kano Zata Gina Masallacin Da Aka Ƙona Masallata A Gezawa