Leadership News Hausa:
2025-11-02@19:51:05 GMT

Sin Na Maraba Da Kamfanonin Kasa Da Kasa Har Da Na Amurka 

Published: 29th, May 2025 GMT

Sin Na Maraba Da Kamfanonin Kasa Da Kasa Har Da Na Amurka 

Yau Laraba, mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Mao Ning, ta bayyana a gun taron manema labarai na yau da kullum cewa, ma’anar dangantakar tattalin arziki da cinikayya tsakanin Sin da Amurka, ita ce cimma moriyar juna da kuma samun nasara tare. Kuma ra’ayin ba da kariya ga cinikayya ba zai samar da mafita ba.

Bangaren Sin yana maraba da kamfanoni daga dukkan kasashe, ciki har da kamfanonin Amurka, da su yi aiki da samun bunkasa a kasar Sin, da zurfafa hadin gwiwa.

Dangane da umarnin da gwamnatin Trump ta bayar ga ofishin jakadancin Amurka, da karamin ofishin jakadancin kasar na dakatar da sabuwar damar bayar da Biza ga daliban waje dake koyon ilmi a kasar kuwa, Mao Ning ta bayyana cewa, kasar Sin na fatan Amurka za ta kare hakki da muradun daliban sassan kasa da kasa, ciki har da daliban kasar Sin.

Bugu da kari, Mao Ning ta ce, domin kara saukaka mu’amalar al’ummun Sin da kasashen ketare, bangaren Sin na kira ga dukkan kasashe mambobin kungiyar GCC da su shigo Sin ba tare da Biza ba. (Safiyah Ma)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace

 

Yayin ganawarsa da firaministan Thailand, Shugaba Xi Jinping ya ce a shirye kasarsa take ta karfafa hadin gwiwa da Thailand kan dabarun samun ci gaba, tare kuma da gabatar da gogewarta na samun ci gaba a sabon zamani, kuma ya yi kira da a gaggauta gina layin dogo tsakanin Sin da Thailand da bunkasa hadin gwiwa a bangaren cinikin amfanin gona da tattalin arziki mai kiyaye muhalli da kuma kirkire kirkiren fasaha. (Mai fassara: FMM)

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC October 31, 2025 Daga Birnin Sin Sin Da Amurka Suna Taimaka Wa Juna Da Samun Wadata Tare October 31, 2025 Daga Birnin Sin Xi Jinping Ya Halarci Kwarya-Kwaryan Taron Shugabannin APEC Na 32 Tare Da Gabatar Da Jawabi October 31, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • A Kan Wa Trump Ke Son Kaddamar Da Hari a Najeriya?
  • Shugaban Kasar Najeriya Ya Mayar Da Martani Ga Takwaransa Na Amurka Akan Rikicin Addini
  • Iran ta damu da halin da ake ciki a yankin El Fasher na Sudan
  • Israila Ta Kai Hari  Kan Ofishin kungiyar UNICEF Dake Gaza A
  • CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka
  • Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace
  • Masar da Eritrea Sun Tattauna Bukatar Tallafawa Kasar Sudan
  • Sin Da Amurka Suna Taimaka Wa Juna Da Samun Wadata Tare
  • NAJERIYA A YAU: Dalilan Da Daliban Makarantar Kudi Suka Fi Na Gwamnati Kokari
  • An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Kirkire-kirkire Da Bude Kofa Da Raba Damar Samun Ci Gaba A Colombo