Leadership News Hausa:
2025-05-30@03:44:50 GMT

Sin Na Maraba Da Kamfanonin Kasa Da Kasa Har Da Na Amurka 

Published: 29th, May 2025 GMT

Sin Na Maraba Da Kamfanonin Kasa Da Kasa Har Da Na Amurka 

Yau Laraba, mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Mao Ning, ta bayyana a gun taron manema labarai na yau da kullum cewa, ma’anar dangantakar tattalin arziki da cinikayya tsakanin Sin da Amurka, ita ce cimma moriyar juna da kuma samun nasara tare. Kuma ra’ayin ba da kariya ga cinikayya ba zai samar da mafita ba.

Bangaren Sin yana maraba da kamfanoni daga dukkan kasashe, ciki har da kamfanonin Amurka, da su yi aiki da samun bunkasa a kasar Sin, da zurfafa hadin gwiwa.

Dangane da umarnin da gwamnatin Trump ta bayar ga ofishin jakadancin Amurka, da karamin ofishin jakadancin kasar na dakatar da sabuwar damar bayar da Biza ga daliban waje dake koyon ilmi a kasar kuwa, Mao Ning ta bayyana cewa, kasar Sin na fatan Amurka za ta kare hakki da muradun daliban sassan kasa da kasa, ciki har da daliban kasar Sin.

Bugu da kari, Mao Ning ta ce, domin kara saukaka mu’amalar al’ummun Sin da kasashen ketare, bangaren Sin na kira ga dukkan kasashe mambobin kungiyar GCC da su shigo Sin ba tare da Biza ba. (Safiyah Ma)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

An Gudanar Da Dandalin Kawancen Birane Na Kasa Da Kasa Na Shanghai 

A yau Alhamis ne aka gudanar da dandalin “Kasa da kasa na tattaunawa tsakanin magadan biranen duniya na Shanghai, da dandalin kawancen birane na kasa da kasa na Shanghai na shekarar 2025.”

Magadan birane da wakilai daga birane 26 dake cikin kawancen, daga sassan kasashen duniya 22, sun hallara a bakin kogin Huangpu, domin tattaunawa, da musaya game da yanayin makomar birane a nan gaba, da hadin gwiwa, inda suka mayar da hankali kan “Bunkasa birane masu korayen itatuwa, da karancin fitar da iskar carbon, da ci gaba da kirkire-kirkire”.

Kazalika a yau din, birnin Shanghai ya sanya hannu kan takardun bunkasa kawance da musaya tare da Tbilisi na Georgia, da Vientiane na Laos da sauransu. A shekarun baya bayan nan, biranen kasa da kasa dake shiga kawance da birnin Shanghai na ta karuwa. Inda ya zuwa yanzu, birnin ya gina kawance tare da birane 95 na kasashe 59 dake fadin duniya. (Mai fassara: Saminu Alhassan)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gasar Wasanni Ta Kasa Wata Hanya Ce Ta Hada Kan Matasan Nijeriya– Obasanjo
  • An Gudanar Da Dandalin Kawancen Birane Na Kasa Da Kasa Na Shanghai 
  • Duniyarmu A Yau: Wasikar Lawyoyi 800 Ga Firay Ministan Kasar Burtaniya Kan Gaza
  • Amurka za ta hana ‘’visa’’ ga daliban dake sukanta a shafukan sada zumunta
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Yayi Tir Da Jakadan Burtaniya A Amurka Dangane Da Tashe Uranim A Kasar
  • Ina Fatan Cigaba Da Taka Leda Har Zuwa Lokacin da Zan Cika Shekara 40 A Duniya – Salah
  • Xi Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Taron Kasa Na Yara Jagorori Na Kasar Sin 
  • Raya Al’adu Wani Sirri Ne Na Ci Gaban Kasar Sin
  • Jama’ar gari sun kashe DPO, sun ƙona ofishin ’yan sanda a Kano