Aminiya:
2025-07-12@01:10:03 GMT

Wike ya rufe ofishin FIRS da Bankin Access kan rashin biyan haraji

Published: 26th, May 2025 GMT

Hukumar Kula da Babban Birnin (FCTA) Tarayya ta rufe ofishin Hukumar Tara Haraji ta Kasa (FIRS) da kuma ginin Bankin Access kan rashin biyan haraji na sama da shekaru 25.

Daraktan Kula da Filaye na Hukumar FCTA, Chijioke Nwankwoeze, ya bayyana cewa hukumar bin ginin da bankin Access yake bashin harajin shekara 35, ofishin FIRS da ke unguwar Wuse Zone 5 kuma bashin harajin shekara 25.

Babban Ofishin na FIRS na daga cikin fitattun gine-gine da Hukumar Tara Kuɗaɗen Haraji na Babban Birnin ta rufe a safiyar Litinin, kan zargin rashin biyan haraji.

Sauran sun  shafa da ginin Bankin Access da da ofishin kamfanin mai Total Energy da fitaccen otel din Ibro Hotel a unguwar Wuse, da sauran wurare 4,700 a Abuja.

Rikici ya barke a taron Atiku da kungiyoyin Arewa NAJERIYA A YAU: Tasirin Dangantakar Bangaren Zartarwa Da Na Majalisa A Kan Talaka

Chijioke Nwankwoeze, ya bayyana cewa ginin bankin Access da matakin ya shafa, mallakin wani wani kamfani ne, inda bankin ta kama haya.

Kazalika hukumar ta kwace izinin mallakar wasu filaye a wasu fitattun unguwanni saboda matsalar rashin biyar harajin.

Daraktan Kula da Bunƙasa Birnin Abuja, Mukhtar Galadima, ya jagoranci aikin ne bayan hukumar ta fitar da sanarwar rashin biyan harajin da ya kamata.

Ya bayyana cewa ana bin kamfanin Total harajin Shekara 10, wanda ya cika a watan Maris na 2025.

Fili mai lamba 2456 da ke titin Cadastral Zone A02, a unguwar Maitama, mallakin Kamfanin Rana Taher Furniture saboda rashin biyan harajin kas ana shekara 34.

Galadima ya bayyana cewa aikin zai ci gaba a sauran unguwannin Abuja, yana mai gargaɗin waɗanda abin ya shafa su gaggauta yin abin da aya kamata, ko su kuka da kansu.

Hukumar FCDA ta tsaurara matakan karbar haraji, musamman kam dokokin da suka shafi gine-gine da mallakar kasa a ƙarƙashin Minista mai ci, Barista Nyesom Wike.

Ya bayyana cewa wajibi ne masu filayen da hukumar ta kwace su tashi nan take, su bi hanyar da ta dace domin warware duk wata matsala.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Haraji rashin biyan haraji ya bayyana cewa

এছাড়াও পড়ুন:

Majalisar Tarayya Ta Karrama NPA Da Kyautar Gaskiya Da Riƙon Amana Ta 2025

Shi ma Shugaban Kwamitin Asusun Jama’a na Majalisar Dattawa, Sanata Ahmed Wadada, ya bayyana cewa wannan kyauta alama ce ta gaskiya da amincewa da ayyukan hukumar.

Ya ce NPA ta nuna ƙwazo wajen bin ƙa’idojin lissafi da kuma tallafa wa hanyoyin bayyana gaskiya a ayyukan gwamnati.

Shugaban NPA, Dr. Abubakar Dantosho, wanda ya karɓi kyautar a madadin hukumar, ya sake tabbatar da ƙudirinsa na yin gyare-gyare da kuma tabbatar da gaskiya a dukkanin ayyukan hukumar.

Dr. Dantosho ya ƙara da cewa yin adalci da riƙon amana wajen harkokin kuɗi na daga cikin abubuwan da gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ke da niyya a ƙarƙashin shirin “Renewed Hope”.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Majalisar Tarayya Ta Karrama NPA Da Kyautar Gaskiya Da Riƙon Amana Ta 2025
  • Malaman Jihar Jigawa Sun Karrama Shugaban Hukumar Alhazai Ta Jihar
  • NPA Ta Yi Wa Ma’aikatanta 1,500 Karin Girma
  • Aragchi: Kofar Iran Ta Tattaunawa A Bude Take, Amma Amurka Sai Ta Biya Kudade Kan Kura-Kuranta
  • Shugaban Kasar Iran Yace Huldar kasar Iran Da IAEA Zai Ci Gaba Ne Idan Ta Daina Fuska Biyu
  • Kwastam ta kama mazaƙutar jakai da aka yi yunƙurin safararsu
  • Gwamna Namadi Ya Bukaci Hadin Gwiwar Hukumar Kwastam Don Farfado Da Yankin Kasuwanci Na Maigatari
  • An gabatar da Ganduje a matsayin shugaban kwamitin hukumar FAAN
  • Hukumar EFCC Ta Kai Wa Yaran Makaranta Yaki Da Rashawa A Ilorin
  • Hukumar Kiyaye Hadura Ta Kasa Za Ta Aiki Da ‘Yan Jarida A Kano