HausaTv:
2025-07-12@01:30:09 GMT

Iran Ta Kira Yi Jakadan Faransa Akan Furucin Ministan Harkokin Wajen Kasarsa

Published: 26th, May 2025 GMT

Ma’aikatar harkokin wajen jamhuriyar musulunci ta Iran ta gayyaci jakadan kasar Faransa dake nan Iran domin nuna masa kin amincewa da furucin ministan harkokin wajen kasarsa da ya shafi batunci ga Iran.

Muhammad Tanhaye wanda shi ne mai kula da bangaren kasashen turai a ma’aikatar harkokin wajen jamhuriyar musulunci ta Iran,  ya bukaci Karin bayani a hukumance dangane da abinda ministan harkokin wajen Faransa Jean Nuel Barrot ya fada akan Iran a yayin bikin ” Cannes” na fina-finai a da wani daga cikin fina-finan Iran ya sami kyauta.

Har ila yau, Tanhaye ya yi suka akan yadda gwamnatin ta Faransa ta yi amfani da bikin fina-finan domin yada manufofinta na siyasa.

Haka nan kuma ya ce; Faransa wacce kasa ce mai goyon bayan ‘yan sahayoniya ba ta da  bakin fada akan batun da ya shafi kyawawan halaye da za ta yi Magana akan hakkin bil’adama balle ta soki wasu kasashe.

Jakadan na Faransa ya yi alkawalin mika sakon na Iran ga gwamnatinsa.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: harkokin wajen

এছাড়াও পড়ুন:

Ba lallai matatun man gwamnati su sake aiki ba har abada a Najeriya – Ɗangote

Shugaban rukunin kamfanonin Dangote, Alhaji Aliko Ɗangote, ya ce yana da shakku a kan ko matatun mai mallakin gwamnatin Najeriya za su ƙara aiki a nan gaba.

Najeriya dai na da matatun mai guda hudu mallakinta a biranen Fatakwal da Warri da Kaduna.

Amma attajirin ya ce matatun man waɗanda ke ƙarƙashin kulawar Kamfanin Mai na Najeriya (NNPCL), sun laƙume sama da Dalar Amurka biliyan 18 wajen gyaransu, amma har yanzu sun ƙi aiki.

Sojoji sun kashe ’yan fashin daji masu yawan gaske a Zamfara Muna so a kafa doka ta bincikar yadda ’yan Nijeriya ke tara dukiya — EFCC

Ɗangote ya bayyana hakan ne ranar Alhamis lokacin da ya karɓi baƙuncin mambobin shugabannin kamfanoni wadanda ke Karatu a Lagos Business School, a rangadinsu a matatar Dangote da ke Legas.

‎Ya ce matatar man shi mai ƙarfin tace ganga 650,000 a kullum yanzu kusan kaso 50 na aikinta a kan tace man fetur ne, yana mai cewa hatta matatun man gwamnati kaso 22 na karfinsu suke sakawa a harkar tace man fetur ɗin.

A cewar attajirin na Afirka, “Mun taɓa sayen matatun man Najeriya daga hannun tsohon Shugaban Kasa Olusegun Obasanjo a watan Janairun 2007.

“Amma lokacin da marigayi Shugaban Kasa Umaru Yar’aduwa ya zo, tsofaffin manajojin matatun sai suka ce masa an sayar da matatun a ƙasa da ainihin ƙimar su a kasuwa, Obasanjo ya ba mu kamar kyauta ne kawai lokacin da zai tafi. Dole sai da muka mayar da su saboda an samu canjin gwamnati.

‎“A lokacin, manajojin matatun sun shaida wa Yar’aduwa cewa matsayin za su tashi, kawai ƙanin kyauta Obasanjo ya ba mu lokacin da zai tafi.

“Yanzu haka maganar da ake yi, an kashe sama da Dala biliyan 18 wajen gyaran su, amma har yanzu ba sa aiki. Kuma ba na tunani, ina da kokwanto a kan yiwuwar sake aikinsu a nan gaba,” in ji shi.

‎Dnagote ya kwatanta ƙoƙarin da ake yi na gyara matatun da na mutumin da ke kokarin zamanantar da motar da ya saya sama da shekaru 40 da suka wuce ne, alhalin zamani ya riga ya wuce wajen.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka
  • Associated Press: Harin Iran Akan Sansanin Amurka Dake Kasar Qatar Ya Lalata Wata Cibiyar Sadarwa
  • Ba lallai matatun man gwamnati su sake aiki ba har abada a Najeriya – Ɗangote
  • Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Ya Yi Allah  Wadai Da Kakaba Takunkumi Kan Jami’ar Majalisar Dinkin Duniya
  • Aragchi: Kofar Iran Ta Tattaunawa A Bude Take, Amma Amurka Sai Ta Biya Kudade Kan Kura-Kuranta
  • An gurfanar da wasu kan zargin kashe matafiya bikin aure a Jos
  • Ministan Tsaron Iran Ya Bayyana cewa: Martanin Da Iran Ta Mayar Ne Ya Sanya Isra’ila Ta Amince Da Tsagaita Wuta
  • Aragchi Ya Tattauna Da Bin Salman Kan Karfafa Zumunci Tsakanin Kasashen Biyu
  • Rizai: Mun Harbo Jirage Kanana Da Manya 80 Na ‘Yan Sahayoniya
  • Rawar Ganin Da BRICS Ke Takawa Wajen Samar Wa Kasashe Masu Tasowa ‘Yanci A Tsarin Gudanar Da Harkokin Kasa Da Kasa