Majalisar Dokokin Jihar Kaduna ta amince da mutum biyu da Gwamna Uba Sani ya aike da sunayen su a tantance su a matsayin Kwamishinoni.

A cikin wata wasika da Gwamna Uba Sani ya aikawa Majalisar Dokokin, ya bukaci a amince da Farfesa Abubakar Sani Sambo a matsayin Kwamishinan Ilimin sai kuma Barrister Gloria Ibrahim a matsayin Kwamishinar Matasa da cigaban jihar.

Shugaban Majalisar Dokokin Jihar Kaduna, RT. Hon. Yusuf Dahiru Liman ya bukaci sabbin kwamishinonin da aka amince da su, su yi amfani da kwarewar su domin farfado da bangaren Ilimi da bunkasa ci gaban matasa.

Da yake ganawa da manema labarai jim kadan bayan tantancewa da amincewa da shi a matsayin Kwamishinan Ilimi, Farfesa Abubakar Sani Sambo ya lashi takobin gudanar da sauye-sauye a bangaren Ilimi ta hanyar fadada damarmaki, da yin garambawul a gine-gine da kuma inganta sha’anin koyarwa a makarantun dake fadin Jihar Kaduna.

Haka nan ita ma Barr. Gloria Ibrahim ta bayyana kudirinta na aiwatar da hangen nesa na Gwamna Uba Sani, na shigar da matasa cikin harkokin Mulki da ci gaba, sannan ta sha alwashin yin aiki tukuru wajen samar da damarmaki ga matasan dake fadin Jihar Kaduna.

 

Shamsuddeen Mannir Atiku

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Kwamishinoni Majalisar Dokokin Jihar Kaduna

এছাড়াও পড়ুন:

Tsaro Ya Inganta A Zamfara, In Ji Gwamna Lawal Yayin Tattakin Zaman Lafiya Na Tarihi A Jihar

Da yake jawabi ga ɗimbin mutanen da suka halarci wannan tattaki, Gwamna Lawal ya jaddada ƙudirin gwamnatinsa na kawar da duk wani nau’in miyagun laifuka a jihar, tare da mai da hankali sosai kan ‘yan bindiga.

Ya ce, “A yau mun fito dubunnan mu domin mu yi tattakin samun zaman lafiya, domin mu sanar da duniya cewa Zamfara ta samu ci gaba sosai ta fuskar tsaro.

“Gwamnatina ta ba da himma da kayan aiki masu yawa don ƙarfafa sojoji, tattara bayanan sirri, da haɗa kai don dawo da zaman lafiya a jihar.

“Mun sami gagarumar nasara a yaƙin da ake yi da ‘yan bindiga, yawancin wuraren da ake fama da rikici a baya, a halin yanzu sun kasance cikin kwanciyar hankali. Hanyoyin da a da ba a iya wucewa, a yanzu matafiya na wucewa lami lafiya cikin ‘yanci.

 

“Kuna iya ganin yadda mutane ke tafiya cikin walwala tare da gudanar da ayyukansu na yau da kullum da kuma yadda suke taruwa cikin farin ciki don yin tattakin samar da zaman lafiya. Wannan ya nuna a fili cewa mutanenmu sun samu zaman lafiya kuma suna son zaman lafiya. Hakan kuma ya nuna cewa jama’a sun fahimta kuma sun yaba da abin da gwamnatin jihar ke yi don inganta zaman lafiya.”

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tsaro Ya Inganta A Zamfara, In Ji Gwamna Lawal Yayin Tattakin Zaman Lafiya Na Tarihi A Jihar
  • Shekaru 6: Don amfanin matasa mun inganta ilimi da noma — Gwamna Buni 
  • Shekaru 6: Don amfanin matasa mun inganta harkokin ilimi, noma — Gwamna Buni 
  • Majalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince Da Dokokin Ilimin Noma da Gyaran Kotunan Gargajiya
  • ’Yan bindiga sun kashe makiyaya 2, sun sace shanu 320 a Kaduna
  • Ko kwabo ban ciyo bashi ba tun da na zama Gwamnan Kaduna – Uba Sani
  • Majalisar Nasarawa Ta Bukaci A Cire Malamai 1000 Daga Aikin Tantancewar Da Ake Yiwa Malamai
  • Adamawa Ta Amince Da Mafi Ƙarancin Albashi Na ₦70,000 Ga Ma’aikatan Ƙananan Hukumomi 
  • Gwamna Uba Sani Ya Kammala Titin Unguwar Su El-Rufai