Gwamnatin Gombe ta rattaba hannu kan kwangilar biliyan 48 na aikin zaizayar Kasa
Published: 29th, May 2025 GMT
Jihar Gombe ta rattaba hannu kan kwangilar sama da biliyan 48 don aikin kula da Makarantar ‘yan mata ta Mega dake Doma da kuma zaizayar kasa
Baya ga sanya hannu kan kwangilar, an kuma bayar da cak don biyan diyya ga mazauna yankin mai nisan mita 10 da ke kan hanyar aikin.
Da yake jawabi a wurin rattaba hannu kan kwangilar a hukumance a Hayin Missau Bogo, Gwamna Inuwa Yahaya ya bayyana matakin a matsayin wani muhimmin mataki na tabbatar da muhallin Gombe da kuma kare makomar jama’a.
A cewarsa aikin ba wai kawai zai shawo kan zaizayar kasa ba ne zai dawo da fata ga al’ummomin da abin ya shafa.
Alh. Inuwa Yahaya wanda ya bada umarnin kammala aikin a cikin watanni 30 ya bukaci dan kwangilar da ya gabatar da aiki mai inganci.
Ya yi kira ga sarakunan gargajiya da shugabannin al’umma da su ci gaba da taka muhimmiyar rawa wajen wanzar da zaman lafiya da juna a tsakanin al’umma, da kuma kiyaye ayyukan da ba su dace ba kamar sare itatuwa da zubar da shara da ke cutar da muhalli.
Shima da yake jawabi kwamishinan albarkatun ruwa da muhalli da gandun daji na jihar Gombe Mal. Muhammad Fawu, ya yabawa hadin gwiwar da gwamnatin Gombe da Bankin Duniya suka yi wajen samar da kudaden aikin, ya ce wani gagarumin kokari ne na kare muhalli da kuma tabbatar da makomar al’umma.
KARSHEN HUDU
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: zaizaiya hannu kan kwangilar
এছাড়াও পড়ুন:
An Kaddamar Da Bikin BIRTV2025 A Beijing
Yau Laraba, aka kaddamar da bikin nune-nunen harkokin rediyo da fina-finai da talabijin na kasa da kasa na Beijing karo na 32 ko kuma BIRTV2025 a Beijing, fadar mulkin kasar Sin, wanda kamfanin CBIC na kasar Sin ya dauki nauyin shiryawa, bisa jagorancin babbar hukumar kula da harkokin rediyo da talabijin ta kasa gami da babban rukunin gidajen rediyo da talabijin na kasa wato CMG.
Bikin na BIRTV2025 yana kokarin kafa wata gada don inganta mu’amala tsakanin kasa da kasa ta hanyar gudanar da harkokin kasa da kasa, ciki har da taron sanin makamar aiki don inganta kwarewar kafafen yada labaran Sin da Afirka, wanda zai mayar da hankali kan irin labaran da suka kamata a watsa, gami da hanyoyin watsa su, tare kuma da lalubo sabbin hanyoyin hadin-gwiwar Sin da Afirka a fannin masana’antun talabijin da rediyo.
Bikin BIRTV2025 na bana wanda za’a rufe shi a ranar 26 ga wata, ya samu halartar kamfanoni sama da 500 daga kasashe da yankuna fiye da 20, wadanda suke nuna sabbin nasarori da fasahohin da suke da su a sana’o’in da suka shafi rediyo da fina-finai da talabijin da kuma intanet. (Murtala Zhang)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp