HausaTv:
2025-06-01@02:01:36 GMT

Tarayyar Turai Ta Yi Barazanar Karin Matsin Lamba Akan “Isra’ila”

Published: 30th, May 2025 GMT

Wasu jami’an diplomasiyyar turai sun yi wa gwamnatin Benjamin Netanyahu da cewa za ta fuskanci Karin matsin lamba idan har ba ta sauya halayyarta akan Gaza ba.

Jaridar “Washington Post” ta Amurka ta ambato jami’an diplomasiyyar turai suna cewa; sabon tsarin da ake yin aiki da shi na raba kayan agaji a Gaza, ya juya ya zama harigitsi kuma ana bude wuta akan mutane da hakan ya yi sanadiyyar jikkatar Falasdinawa da dama.

Har ila yau jami’an diplomasiyyar na turai sun ce, ko kadan ba su da aniyar bayar da kayan agajinsu ga masu tafiyar da tsarin da su ne Isra’ila da Amurka.”

 Bugu da kari, majiyar diplomasiyyar ta tarayyar turai ta ci gaba da cewa; Hotunan masu ban tsoro da suke fitowa daga Gaza, sun kai musu iya wuya, ba za su iya ci gaba da jurewa ganinsu ba.”

A cikin kwanakin bayan nan dai kasashen turai sun fara yin matsin lamba akan HKI da ta bari a shigar da kayan agaji cikin yankin na Gaza da kuma yadda take ci gaba da kashe fararen hula da kuma rusau din da take yi mai yawa.

A karon farko, tun kirkirar HKI, kasar Jamus ta soki siyasar Tel Avi akan Gaza, da hakan yake nuni da yadda kasashen turai din suke kara matsin lamba.

Shugaban gwamnatin jamus  Friedrich Merz ya ce; Harin da Isra’ila ta kai wa wata makaranta a Gaza, ya tashi daga karkashin fada da ta’addanci, ya zama wani abu daban.”

A can kasar ta jamus din dai jam’iyyar hamayya ta ” Green Party” ta ce; bai kamata a rika amfani da makaman kasar Jamus a yakin Gaza ba.”

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Mai Ba Da Shawara Ga Jagora Ya Mayar Da Martani Ga Barazanar Trump Kan Cibiyoyin Nukiliyar Iran

Mai ba da shawara ga jagoran juyin juya halin Musulunci ya mayar da martani ga barazanar shugaban kasar Amurka kan cibiyoyin makamashin nukiliyar Iran

Ali Shamkhani mashawarcin Jagoran juyin juya halin Musulunci a fagen siyasa ya jaddada cewa: Iran kasa ce mai cin gashin kanta mai tsayayyen tsarin tsaro, al’umma masu tsayin daka, da jajayen layi. Ya jaddada cewa, “tattaunawa hanya ce ta ci gaba da kuma kiyaye moriyar kasa da mutunci, ba kayan aiki na tilastawa ko mika wuya ba.”

Shamkhani ya rubuta a shafinsa na dandalin X cewa: “Burin isa ga cibiyoyin nukiliyar Iran da kuma ‘tarwatsa su’ ba komai ba ne illa mafarki da shugabannin Amurka da suka gabata sun kasance sun yi has ashen hakan.

Ya kara da cewa: Iran kasa ce mai cin gashin kanta, mai tsarin tsaro mai karfi, mutane masu juriya da jajayen layi. Ya kuma jaddada cewa tattaunawa ita ce hanyar samun ci gaba da kuma kiyaye moriyar kasa da mutunci, ba tilastawa ko mika wuya ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Macron : Faransa za ta iya sanya takunkumi ga gwamnatin Isra’ila matukar ba ta kawo karshen killace Gaza ba
  • Hana shigar da abinci da Isra’ila ta yi zuwa Gaza ‘laifi ne na yaki’: MDD
  • MDD: Yankin Gaza Ne Ya Fi Ko’ina Fama Da Yunwa A Doron Kasa
  • Mai Ba Da Shawara Ga Jagora Ya Mayar Da Martani Ga Barazanar Trump Kan Cibiyoyin Nukiliyar Iran
  • Sojojin Yemen Sun Hana Jigilar Jiragen Sama A Isra’ila Tare Da Firgita ‘Yan Sahayoniyya
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Aiwatar Da Kisan Kiyashi Kan Falasdinawa A Yankin Zirin Gaza
  •  Fiye Da Falasdinawa 60 Ne Su Ka Yi Shahada A Jiya Laraba
  •  Yemen: Wuce Gona Da Irin HKI Ba Zai Sauya Mana Ra’ayi Akan Ci Gaba Da Taimaka Wa Gaza Ba
  •  Kasar Chile Na Shirin Yanke Alakar Diplomasiyya Da “Isra’ila”