HausaTv:
2025-05-27@18:29:28 GMT

Sojojin HKI Suna Ci Gaba Da Kai Wa Yankunan Gaza Hare-hare

Published: 27th, May 2025 GMT

Da safiyar yau Talata ne dai sojojin HKI su ka kai wa gabashin zirin Gaza da kuma Khan-Yunus hare-hare, bayan sa’oi daga kisan kiyashin da su ka yi wanda ya ci rayukan mutane 80.

Saandiyyar sabon harin na safiyar yau, wani karamin yaro ya yi shahada, a yankin al-karama dake Arewacin Gaza.

A daren jiya ma dai sojojin na HKI sun kai wasu hare-haren a unguwar ” Zaytun” dake gabashin Gaza.

Tashar talbijin din ‘al-Aqsa” ta bayar da labarin dake cewa; Unguwar Shuja’iyya’ da wasu unguwannin a gabashin birnin Gaza sun fsukanci hare-haren ‘yan sahayoniya daga manyan bindigogi.

Wasu hare-haren na ‘yan sahayoniya sun shafi Arewacin zirin Gaza da su ka yi sanadin rushewar gidaje, haka nan kuma asibitocin da su ka saura su ma sun fuskanci irin wadannan hare-haren.

Wasu kafofin Falasdinawa sun ce an kai gawar wani shahidi a yankin Deir-Balah.

Wasu Falasdinawan sun watsa bidiyo din gobarar da ta tashi saboda harin na ‘yan sahayoniya a jiya, wacce kuma har zuwa yau ba ta mutu ba.

Tashar talabijin “al-Aqsa” ta kuma bayar da labarin dake cewa; kananan jiragen ruwan HKI sun hude wuta a yankin “Mawasi” wanda yake cike da ‘yan hijira a yammacin Khan-Yunus.

Sa’oi kadan da su ka gabaci wannan harin, ‘yan sahayoniyar sun kira yi mutanen yankin da su fice daga gidajensu domin rushe su.

Likitocin da suke yankin sun sanar da tashar talabijin din ‘Al-jariza’ cewa mutane 80 ne su ka yi shahada, fiye da 30 daga cikinsu daga makarantar ‘Fahmi al-jarjawi’ da unguwar “Darj” cikin Birnin Gaza.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Sin Za Ta Harba Na’urar Binciken Samaniya Ta Tianwen-2

Yanzu haka ana ci gaba da gudanar da shirye-shirye, domin harba na’urar binciken samaniya ta kasar Sin mai lakabin Tianwen-2, a ranar Alhamis 29 ga watan nan, na’urar da ake fatan za ta samar da bayanai game da sirrin dake tattare da tauraron dake kusa da sararin samaniyar bil adama, da karamin tauraron dake kewaya da’irar dake shiyyar, kamar dai yadda hukumar kula da binciken sararin samaniya ta kasar Sin ko CNSA ta sanar a Litinin din nan.

Ana sa ran na’urar Tianwen-2, za ta tattaro samfura daga tauraro mai lamba 2016HO3, aikin da zai zamo irinsa na farko a fannin, kana zai kewaya karamin tauraron “comet 311P”.

Yanzu haka dai ana ci gaba da shirye-shirye domin tabbatar da nasarar harba na’urar Tianwen-2, daga cibiyar harba kumbuna ta Xichang a lardin Sichuan na kudu maso yammacin kasar Sin. (Mai fassara: Saminu Alhassan)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojojin Yahudawa sun Kashe Wani Matashi A Yankin Yamma Da Kogin  Jordan
  •  Sojojin Yemen Sun Sake Kai Wa HKI Hari Da Makami Mai Linzami
  • Sin Za Ta Harba Na’urar Binciken Samaniya Ta Tianwen-2
  • Falasdinawa 30 sun yi shahada a Wani harin Isra’ila kan wata makaranta
  • Hare-Haren HKI Kan Wata Makaranta A Gaza Ya Kashe Mutane 46 Daga Ciki Harda Yara Kanana
  •  Sojojin HKI Sun Yi Wani Sabon Kisan Kiyashi A Gaza
  • Mene Ne Dalilin Amurka Na Cewa Zata Harba Makamamin Nukiliya Kan Yankin Zirin Gaza?
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Suna Ci Gaba Da Kai Hare-Haren Wuce Gona Da Iri Kan Birnin Tul-Karam Na Falasdinu
  • ‘Yar Majalisar Dokokin Ireland Ta Yi Suka Kan Shugabannin Turai Tare Da Neman Afuwa Daga Falasdinawa