Sojojin HKI Suna Ci Gaba Da Kai Wa Yankunan Gaza Hare-hare
Published: 27th, May 2025 GMT
Da safiyar yau Talata ne dai sojojin HKI su ka kai wa gabashin zirin Gaza da kuma Khan-Yunus hare-hare, bayan sa’oi daga kisan kiyashin da su ka yi wanda ya ci rayukan mutane 80.
Saandiyyar sabon harin na safiyar yau, wani karamin yaro ya yi shahada, a yankin al-karama dake Arewacin Gaza.
A daren jiya ma dai sojojin na HKI sun kai wasu hare-haren a unguwar ” Zaytun” dake gabashin Gaza.
Tashar talbijin din ‘al-Aqsa” ta bayar da labarin dake cewa; Unguwar Shuja’iyya’ da wasu unguwannin a gabashin birnin Gaza sun fsukanci hare-haren ‘yan sahayoniya daga manyan bindigogi.
Wasu hare-haren na ‘yan sahayoniya sun shafi Arewacin zirin Gaza da su ka yi sanadin rushewar gidaje, haka nan kuma asibitocin da su ka saura su ma sun fuskanci irin wadannan hare-haren.
Wasu kafofin Falasdinawa sun ce an kai gawar wani shahidi a yankin Deir-Balah.
Wasu Falasdinawan sun watsa bidiyo din gobarar da ta tashi saboda harin na ‘yan sahayoniya a jiya, wacce kuma har zuwa yau ba ta mutu ba.
Tashar talabijin “al-Aqsa” ta kuma bayar da labarin dake cewa; kananan jiragen ruwan HKI sun hude wuta a yankin “Mawasi” wanda yake cike da ‘yan hijira a yammacin Khan-Yunus.
Sa’oi kadan da su ka gabaci wannan harin, ‘yan sahayoniyar sun kira yi mutanen yankin da su fice daga gidajensu domin rushe su.
Likitocin da suke yankin sun sanar da tashar talabijin din ‘Al-jariza’ cewa mutane 80 ne su ka yi shahada, fiye da 30 daga cikinsu daga makarantar ‘Fahmi al-jarjawi’ da unguwar “Darj” cikin Birnin Gaza.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
HKI: Sojoji 62 Ne Su Ka Halaka A Gaza A Cikin Wannan Shekara Ta 2025
Jaridar HKI ta “Haaretz'” ta buga labarin da yake cewa: A cikin wannan shekarar ta 2025, sojojinsu da su ka halaka sun kai 62.
A cikin watannin bayan nan an sami karuwar sojojin mamayar da ‘yan gwgawarmaya suke kashewa a Gaza.
Yankin Khan Yunus dake Arewacin Gaza da HKI take riya cewa ta nike shi, sannan kuma ta kori Falasdinawa daga cikinsa, yana daga cikin wuraren da aka yi wa sojojin mamayar kwanton bauna.
Bugu da kari, har yanzu ‘yan gwgawarmayar suna ci gaba da harba makamai masu linzami daga Gaza zuwa matsugunan ‘yan share wuri zauna da suke kusa da Gaza.
A jiya ma dakarun “Sarayal-Quds” na kungiyar Jihadul-Islami ta sanar da harba makamai masu linzami zuwa matsugunan da suke da Gaza.
Jaridar ta “Haaratz’ ta kuma ce, Fira ministan na HKI bai yi wa iyalan ko daya daga cikin iyalan sojojin da aka kashe a Gaza ta’aziyya ba, balle ya gana da su.
Jaridar ta kuma ce, hotunan da ake nunawa na Netanyahu yana ganawa da iyalan sojoji tsoho ne ba sabo ba ne.