Jami’ar Jos ce ta zama gwarzon gasar wasannin ma’aikatan jami’o’in Nijeriya karo na 14 (NUSSA), wadda Jami’ar Bayero da ke Kano ta karɓi bakuncinta. Jami’ar ta Jos ta lashe lambobin yabo guda 13, ciki har da Zinare 7, Azurfa 3 da Tagulla 3, wanda ya ba ta damar darewa saman teburin nasarori.

A matsayi na biyu kuma, Jami’ar Ahmadu Bello, Zaria, ta samu nasarar lashe lambobin yabo 12 – zinare 6, azurfa 3 da tagulla 3.

Jami’ar Tarayya ta Dutsinma ta zo ta uku da zinare 4, azurfa 4 da tagulla 5.

Gasar Wasanni Ta Kasa Wata Hanya Ce Ta Hada Kan Matasan Nijeriya– Obasanjo Kyawawan Halayen Annabawa Da Ke Nuni Da Cikarsu (AS)

Babban abin da ya dauki hankali a gasar karshe da aka gudanar a ranar Juma’a, 30 ga Mayu, 2025, shi ne wasan karshe na kwallon kafa tsakanin Jami’ar Tarayya ta Harkokin Sufuri, Daura da Jami’ar Tarayya, Dutsinma. Bayan wasan ya kare 1-1, FUT Daura ta doke Dutsinma da ci 3-1 a bugun fenareti, inda ta lashe zinaren kwallon kafa.

Wannan gagarumar nasara da Jami’ar Jos ta samu na kara tabbatar da jajircewar jami’ar wajen bunkasa wasanni a tsakanin ma’aikata, da kuma karfafa dankon zumunci da kwarewa a tsakanin jami’o’in kasar nan.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Wasanni

এছাড়াও পড়ুন:

‘Yan Wasan Kano Sun Rasu Sanadiyar Hadarin Mota Yayin Dawowa Daga Gasar Wasanni Ta Kasa

Aƙalla ‘yan wasa 20 daga tawagar jihar Kano ne suka rasu, yayin da da dama suka jikkata,  sakamakon mummunan hatsarin mota da ya faru a gadar Dakatsalle, sa’ilin da suke dawowa daga Gasar Wasanni ta Kasa da aka kammala kwanan nan a Abeokuta.

Shugaban Hukumar Wasanni ta Jihar Kano, Umar Bala Fagge, ya tabbatar da faruwar lamarin.

Ya bayyana cewa motar da ke ɗauke da ‘yan wasan, wadda ke ɗauke da mutane 30, ta faɗa gadar ta Dakatsalle da ke jihar ta Kano.

“Yayin da nake magana da ku yanzu, mun kirga gawarwaki 19,” ya fada cikin tashin hankali.

Ado Salisu, tsohon Mataimakin Shugaban Kungiyar ‘Yan Jarida da ke kula da lamuran Wasanni ta Najeriya (SWAN), ya ce an kai waɗanda suka jikkata babban asibitin gwamnati da ke Kura.

Daga cikin waɗanda suka rasu akwai ɗan Salisu Jegu, ɗan jarida a fannin wasanni na gidan rediyon Express Radio.

Daga Khadijah Aliyu

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ‘Yan Wasan Da Tauraruwar Ronaldo Da Messi Ta Hana Su Haskawa
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Kutsa Cikin Yankunan Kasar Siriya Tare Da Kafa Wuraren Bincike
  • An Karrama Dalibar Kaduna Da Ta Zo Ta Biyu A Gasar Karatun Alkur’ani Ta Duniya
  • Ministocin Wajen Sin Da Kamaru Sun Gana Kan Alakar Kasashensu Da Batun Kafa IOMed
  • Nijeriya Ta Lashe Gasar Unity Cup Bayan Doke Jamaica A Bugun Fenarati
  • ‘Yan Wasan Kano Sun Rasu Sanadiyar Hadarin Mota Yayin Dawowa Daga Gasar Wasanni Ta Kasa
  • Tarayyar Turai Ta Yi Barazanar Karin Matsin Lamba Akan “Isra’ila”
  • An gano gawar direba a cikin mota a Bayelsa
  • Gasar Wasanni Ta Kasa Wata Hanya Ce Ta Hada Kan Matasan Nijeriya– Obasanjo