Sojojin mamayar Isra’ila na ci gaba da kai hare-haren wuce gona da iri kan birnin Tulkaram da sansanoninsa da ke gabar yammacin kogin Jordan

Sojojin mamayar Isra’ila na ci gaba da kai hare-hare kan birnin Tulkaram da sansanoninsa a rana ta 119 a jere, da kuma sansanin Nour Shams a rana ta 106, a daidai lokacin da sojojin suke ci gaba da tsananta kai hare-hare kan yankuna Falasdinawa da kuma kma su tare da yinawungaba da su zuwa wuraren da baa san ko’ina ba ne.

Da sanyin safiyar Lahadi ne sojojin mamayar Isra’ila suka kai farmaki gidan Essam Odeh, sakataren kungiyar hadin kan iyalan shahidai da ke yankin kudancin Falasdinu, inda suka kama shi da diyarsa Sarah mai shekaru 20 bayan an yi musu tambayoyi. An saki Issam Odeh, yayin da sojojin mamayar suka tafi da diyarsa Sarah, da nufin matsawa dansa Amir ya mika kansa. Idan dai ba a manta ba, an sha tsare Issam Odeh, sannan kuma an tsare ‘ya’yansa biyu Muhammad da Isma’il a gidan yari na tsawon watanni ba tare da gurfanar da su a gaban kotu ba.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: mamayar Isra ila kai hare hare

এছাড়াও পড়ুন:

Qalibof: Asarorin HKI A Yakin Kwanaki 12 Yafi Abinda Ta Bayyana

shugaban majalisar dokokin kasar Iran Mohammad Baqir Qalibof ya bayyana cewa asarorin da HKI ta yi a yakin kwanaki 12 da JMI suna da yawa. Kuma babu shakka ya fi abinda ta bayyana.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto shugaban majalisar dokokin kasar ta Iran yana fadar haka a lokacinda yake hira da wata tashar talabijin a nan Tehran . Ya kuma kara da cewa. Maganar cewa uahudawa 3500 kawai suka ji rauni a yakim gaba daya karya ce.

Qalibof ya ce yana da tabbacin cewa yahudawa akalla 500 suna halaka sanadiyyar hare-haren da sojojin Iran suka kai a kan HKI a yankin kwamaki 12. .

Ya ce sojojin yahudawan sun saba boye yawan mutanen da suka halaka a yake-yaken da take fafatawa da masu gwagwarmaya a yankin. suna kuma hana yada hutunan bidyo na asarorin da suka yi a yaki. masili daga cikin wasu da dama shi ne yadda suka hada yar rahoton tashar talabijin ta Aljazeera daukar hotuna a yakin saboda basa son muatane su san gaskiya. su kuma ga irin yawan asarorin da suka yi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Qalibof: Asarorin HKI A Yakin Kwanaki 12 Yafi Abinda Ta Bayyana
  • HKI Ta Ci Gaba Da Kai Hare-Hare Kan Kudancin Kasar Lebanon
  •  Masu Kare Hakkin Dan’adam Suna Allawadai Da Takunkumin Amurka  Akann Jami’ar MDD A Falasdinu
  • Shugaban Majalisar Shawarar Musulunci  ya Bayyana Yadda Iran Da Mayar Da Martani Mai Gauni Kan Isra’ila
  • Gwamnatin Mamayar Isra’ila Ta Amince Iran ta Kai Hare-Hare Kan cibiyoyin Sojojinta Guda Biyar
  • Kakakin Hafsan Hafsoshin Sojin Iran Ya Ce: Iranta Dorawa Amurka Alhakin Duk Harin Da Ta Fuskanta
  • ‘Yan Gwagwarmayar Falasdinu Sun Halaka Sojojin Mamaya Biyar Tare Da Jikkata Wasu Goma Na Daban
  • Kakakin Rundunar Izzuddeen Qassam ya Bayyana Yadda Suka Yi Kofar Rago Ga Sojojin Mamayar Isra’ila
  • Falasdinawa 13 Ne Suka Yi Shahada Wasu Da Dama Suka Jikkata A Hare-Haren Sojojin Mamayar Isra’ila A Gaza
  • Gwamnatin Kasar Iran Ta Yi Allawadai Da Hare-Haren HKI Kan Kasar Yemen