Aminiya:
2025-10-16@01:23:27 GMT

Bashin da ake bin Najeriya zai koma tiriliyan 162

Published: 28th, May 2025 GMT

Idan har Majalisar Dokoki ta Kasa ta amince da bukatar Shugaban Kasa Bola Tinubu ta neman sake ciyo sabon bashi, jimillar bashin da ake bin Najeriya a yanzu zai koma Naira tiriliyan 162.

A ranar Talata ce shugaban ya aike wa Majalisar Wakilai takardar neman ta sahale masa ya ciyo bashin, wacce shugaban majalisar, Abbas Tajuddeen ya karanta a zauren majalisar.

Abbas ya ce rancen na 2025–2026, ya kunshi Dala biliyan 21.5 (kimanin Naira tiriliyan 34) da Yuro biliyan 2.2 (kimanin Naira tiriliyan 3.96) da Yen na Japan biliyan 15 (kimanin Naira biliyan 164.7) da kuma Yuro miliyan 65 (kimanin Naira biliyan 116.79) a matsayin tallafi.

Tinubu zai ciyo bashin Naira tiriliyan 39 daga kasashen waje Kotu ta ci su El-Rufa’i tarar miliyan 900

Yana kuma neman cin bashin cikin gida ta hanyar bayar da takardun lamuni na Dala biliyan biyu, kimanin Naira tiriliyan 34.285, don biyan basussukan fanshon adashi gata da suka taru.

Tinubu ya nemi amincewa da bayar da takardun lamuni na Naira biliyan N757.98 a cikin gida domin biyan basussukan fansho da suka taru har zuwa ranar 31 ga Disamba, 2023.

Shugaban kasan ya bayyana cewa an tsara neman bashin ne don tallafa wa muhimman ayyukan a fannonin ababen more rayuwa, noma, lafiya, ilimi, da tsaro a dukkan jihohi 36 da Babban Birnin Tarayya.

Ya bayyana cewa bayar da takardun lamuni na Dala biliyan biyu ya yi daidai da Dokar Zartarwa ta Shugaban Kasa da nufin samar kuɗin domin farfado da darajar Naira da gudanar da muhimman ayyukan samar da ababen more rayuwa da samar da ayyukan yi.

Tinubu ya jaddada gaggawar buqatar wadannan kudade, yana mai nuni da tasirin cire tallafin mai da raguwar kudaden shiga na cikin gida.

Ya lura cewa hakan zai magance rashin bin tanade-tanaden Dokar Gyara Fansho a baya saboda matsalolin samun kuɗi, da nufin dawo da ƙwarin gwiwa a tsarin fansho da inganta jin daɗin tsofaffin ma’aikatan gwamnati.

Dukkan buƙatun guda uku an miƙa su ga Kwamitin Kula da Kuɗi na Majalisar don ɗaukar matakan majalisa na gaba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Najeriya Naira tiriliyan kimanin Naira

এছাড়াও পড়ুন:

Jihar Kano Na Aikin Gyaran Cibiyoyin Lafiya Da Za Su Yi Gogayya Da Na Ƙasashen Duniya

Shugaban Hukumar Kula da Asibitoci ta Jihar Kano (HMB), Dakta Mansur Mudi Nagoda, ya kai ziyarar ba-zata ta duba aiki a Asibitin karbar Haihuwa na Imamu Wali, na Marmara, da kuma Asibitin Sabon Bakin Zuwo.

Ya kai ziyarar ce domin tabbar bin umarnin Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, na wucin gadi wajen sauya wuraren gudanar da ayyukan karbar haihuwa da na yara zuwa wasu cibiyoyi daban.

A karkashin wannan umarni, an mayar da sashen haihuwa na Asibitin Koyarwa na Muhammad Abdullahi Wase zuwa Asibitin Haihuwa na Imamu Wali, yayin da aka mayar da ayyukan yara kyauta da ake yi a Asibitin Yara na Hasiya Bayero zuwa Asibitin Haihuwa na Marmara.

Wadannan canje-canjen sun biyo bayan ci gaba da gyare-gyare da sabunta wadannan asibitoci, wani muhimmin bangare na hangen nesa na Gwamna Yusuf wajen inganta cibiyoyin lafiya a Kano zuwa matakin kasashen duniya da suka ci gaba.

Domin tabbatar da ci gaba da bayar da ayyuka ba tare da tangarda ba, ma’aikatan sassan da abin ya shafa suma an tura su zuwa sabbin wuraren da aka kebe musu.

Yayin ziyarar, Dakta Nagoda tare da daraktoci da ma’aikatan hukumar, ya jaddada muhimmancin bin umarnin gwamnati yadda ya kamata, tare da yabawa shugabanci da ma’aikatan asibitocin da aka ziyarta saboda hadin kai da jajircewarsu.

Ya kara tabbatar da kudirin hukumar wajen tabbatar da cewa bayar da ayyukan lafiya a Jihar Kano zai ci gaba da kasancewa cikin sauki, da inganci, tare da mayar da hankali kan marasa lafiya, duk da gyare-gyaren da ake yi.

 

Daga Khadijah Aliyu

 

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yajin Aikin: Ɗalibai Sun Bai Wa ASUU Da Gwamnatin Tarayya Wa’adin Kwana 7 Su Warware Rikicinsu
  • Jihar Kano Na Aikin Gyaran Cibiyoyin Lafiya Da Za Su Yi Gogayya Da Na Ƙasashen Duniya
  • 2027: Babu Ɗan Siyasar Da Zai Iya Ƙalubalantar Tinubu — Fadar Shugaban Ƙasa
  • Shugaba Tinubu Ya Taya Super Eagles Murnar Samun Cancantar Shiga Gasar Kwallon Kafa Ta Duniya
  • Majalisar Dinkin Duniya Ta Bayyana Cewa: Sake Gina Gaza Zai Ci Dala Biliyan 70
  • Gwamnan Enugu Peter Mbah da kwamishinoninsa sun koma APC
  • Rashin Tsaro A Nijeriya Ba Zai Ƙare Ba Matuƙar Ba A Samar da Ayyukan Yi Da Mulki Na Adalci Ba – Amaechi
  • NAJERIYA A YAU: Shin Babu Wata Hanyar Magance Matsalolin ASUU Ne Sai Ta Yajin Aiki?
  • Hukumar Kwastam Ta Tara Naira Biliyan ₦658.6 A Watan Satumba — DG Na NOA
  • Hada-Hadar Cinikayyar Waje Ta Sin Ta Karu Da Kaso 4% Cikin Watanni Tara Na Farkon Bana