Shugaban kasar Iran wanda ya karbi bakuncin Fira ministan Pakistan da marecen jiya Litinin, ya bayyana cewa; Kasar Pakistan, makwabciyar jamhuriyar musulunci da muhimmanci, ta dubban shekaru.

Shugaban kasar ta Iran Mas’ud Fizishkiyan wanda yake Magana a lokacin taron manena labaru na hadin gwiwa da Fira ministan na Pakistan, ya kuma ce; Da akwai haduwar mahanga a tsakanin kasashen biyu akan batutuwa masu yawa da su ka shafi wannan yankin da kuma duniyar musulunci da kuma a fagen siyasar kasa da kasa.

Shugaba Mas’ud Fizishkiyan ya kuma ce: “A yayin ganawar da mu ka yi da dan’uwana Fira minisan Pakistan da tawagar da taek tre da shi, mun jaddada yadda za a bunkasa alaka ta siyasa, tattalin arziki da al’adu.”

Da yake yin ishara akan aiwatar da yarjeniyoyin da aka kulla a baya a tsakanin kasashen biyu, shugaban kasar ta Iran ya bayyana cewa: Bangarorin biyu za su aiwatar da yarjeniyoyin da su ka kulla a baya, kuma yana cikin abubuwan da mu ka tattauna akai.”

A nashi gefen, Fira ministan na kasar Pakistan Shahbaz Sharif ya yi godiya ga shugaban kasar ta Iran wanda a makwannin da su ka gabata ya kira shi, domin nuna damuwarsa akan halin da ake ciki a yankin-na rikicin kasar da Indiya.”

Haka nan kuma ya bayyana yadda kasar Pakistan ta sami nasara a yakin da ta yi da Indiya, ya kuma ambaci yadda al’ummar kasar ta Pakistan su ka nuna goyon bayansu ga sojojin kasar tasu.

Haka nan kuma bangarorin biyu sun nuna takaicinsu abinda yake faruwa a Gaza, tare da yin kira a kawo karashen yakin da shigar da kayan agaji, haka nan kuma hukunta ‘yan sahayoniyar da su ka tafka laifukan yaki.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Manazaecin Kasar Amurka Ya Ce; Isra’ila Ta Sha Kashi A  Yakinta Da Jamhuriyar Musulunci Ta Iran

Wani manazarci na Amurka ya bayyana sansanonin gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila da Iran ta kaiwa hare-hare

Wani manazarci Ba’amurke ya tattara jerin sansanonin da Iran ta kai wa hare-harer a wata makala inda ya bayyana cewa: Iran ta samu nasara a yakin da ta yi da ‘yan sahayoniyya.

Wani mai sharhi kan harkokin siyasa da ke zaune a birnin Washington Mike Whitney ya yi nazari kan dalilan da ba a bayyana dalilan da suka sa Iran ta yi nasara kan haramtacciyar kasar Isra’ila ba a yakin kwanaki 12 a wani bincike da ya gudanar.

Yana mai cewa; “Me yasa ba zato ba tsammani gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila ta amince da tsagaita bude wuta da Iran?” Whitney ta rubuta a cikin wannan bincike a cikin mujallar Bincike ta Duniya. “Wannan tambaya ce da kafafen yada labarai na Yamma ba su amsa ba, da ke sanya al’ummar Amurka cikin duhu. Watakila kun ji cewa tsaron sararin samaniyar Isra’ila na gab da rugujewa, lamarin da ya bar ta cikin hadari ga hare-haren Iran, amma wannan wani bangare ne na labarin kawai.

Ya kara da cewa: Kasa da makonni biyu da fara wannan rikici, gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila ta mika wuya, Iran tana lalata muhimman wuraren a Isra’ila daya bayan daya bisa zurfin tunani da karfi, ba tare da nuna wata alamar ja da baya ba, don haka Isra’ila ba ta da wani zabi illa amincewa da shan kaye.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • 2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a
  • Associated Press: Harin Iran Akan Sansanin Amurka Dake Kasar Qatar Ya Lalata Wata Cibiyar Sadarwa
  • Shugaban Kasar Iran Yace Huldar kasar Iran Da IAEA Zai Ci Gaba Ne Idan Ta Daina Fuska Biyu
  • Shugaban Yahudawan Iran Ya Tuhumi Isra’ila Da Fakewa A Karkashin Addini
  • Kwamandan Sojin Iran Ya Jaddada Kare Kan Iyakokin Jamhuriyar Musulunci Ta Iran
  • Manazaecin Kasar Amurka Ya Ce; Isra’ila Ta Sha Kashi A  Yakinta Da Jamhuriyar Musulunci Ta Iran
  • Aragchi Ya Tattauna Da Bin Salman Kan Karfafa Zumunci Tsakanin Kasashen Biyu
  • Abdullahi Ojlan Ya Sanar Da Kawo Karshen Fada Da Makami
  • Mai Tsoron Ta Mutu, Shi Yake Maho
  • DAGA LARABA: Shin Ko Zafin Nema Na Kawo Samu?