FCTA ta rufe hedikwatar PDP saboda rashin biyan haraji
Published: 26th, May 2025 GMT
Hukumar Kula da Birnin Tarayya (FCTA), ta rufe hedikwatar jam’iyyar PDP da ke unguwar Wuse a Abuja.
Lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 2:05 na ranar Litinin.
Wike ya rufe ofishin FIRS da Bankin Access kan rashin biyan haraji Ana zargin wani mutum da kashe ɗan maƙwabtansa a SakkwatoJami’an FCTA sun isa ginin tare da jami’an tsaro, inda suka rufe ofishin.
Wasu ma’aikata sun nuna rashin jin daɗinsu, bayan tafka sa-in-sa na tsawo mintuna 15, jami’an FCTA sun bar ma’aikata su fitar da motoci da kayayyakinsu kafin kulle ginin.
A makon da ya gabata, FCTA ta sanar da cewa za ta ƙwace sama da kadarori 4,700 a Abuja saboda rashin biyan haraji na tsawon shekaru 10 zuwa 43.
Waɗannan kadarorin suna yankunan Central Area, Garki, Wuse, Asokoro, Maitama da Guzape.
FCTA, ta ce mallakar waɗannan filaye ya koma hannun gwamnati.
Tun daga Litinin, gwamnati ta fara ƙwace su ba tare da la’akari da wanda ya mallaki kadarar ba.
Daraktan Sashen Kula da Ci Gaban Birnin Tarayya, ya ce za a rufe waɗannan gine-gine kuma ba za a bari kowa ya shiga ba.
Ya ƙara da cewa gwamnati za ta yanke hukunci kan yadda za a yi da su a nan gaba.
Daraktan Sashen Filaye, ya bayyana cewa babu wani hukuncin kotu da ya hana FCTA ɗaukar matakin da ta ke ɗauka a yanzu, don haka za su ci gaba da yin aikinsu.
Ya kuma ce suna tantance kadarorin da suka daɗe ba su biya haraji ba daga shekara ɗaya zuwa 10, kuma za su ɗauki mataki bayan sun kammala tantancewar.
Tun a watan Maris, 2025 FCTA, ta sanar da soke takardun mallakar filaye guda 4,794 saboda rashin biyan haraji, inda ta gargaɗi cewa za ta fara karɓe ikon mallakar filayen daga ranar Litinin.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Babban Birnin Tarayya Haraji Kadarori rashin biyan haraji
এছাড়াও পড়ুন:
NPA Da Ƙungiyar Injiniyoyi Ta Yi Haɗaka Don Bunƙasa Tashoshin Jiragen Ruwa
Oguntala ta bayyana cewa, ana sa ran babban ministan ma’aiktar bunkasa tattalin arziki na teku Mista Adegboyega Oyetola, zai halarci taron, wanda aka tsara za a gudanar a watan Disambar wannan shekarar a garin Ibadan.
Ta bukaci hukumar ta Hukumar kula da Tashoshin Jiragen Ruwa ta Kasa NPA, da ta yi hadaka da kungiyar domin gudanar da taron wanda ta sanar da cewa, Shugaban Hukumar ta NPA Dakta Abubakar Dantsoho ne, zai kasance babban mai gabatar da jawabi, a wajen taron kungiyar.
Kazalika, ta yi kira ga Hukumar ta NPA, da ta dauki nauyin manyan kasidun da za a gabatar da wajen taron tare da samar da ilimi kan batun da ya shafi fannin na bunkasa tattalin arziki na teku.
Shugabar ta kuma bai wa hukumar ta NPA damar da ta yi bajin koli a yayin gudnar da taron, inda kuma ta sanar wa da hukumar ta NPA cewa, ta zabo wasu daga cikin injiniyoyin NPA da ta sanya a cikin kwamtin shiye-shiyen gudanar da taron.
Ta kuma shedawa Dantsoho cewa, wasu masu masana’antu da wasu daga bangaren gwamnati da kuma wasu daga bangaren manyan makarantun kasar nan, na da burin yin hadaka da hukumar ta NPA.
“Mun sa irin kokarin da shugaban hukumar ta NPA key i, musaman wajen kara bunkasa tattalin azrikin da ke a fannin ayyukan Tashoshin Jitagen Ruwan kasar” .
“Muna sane da cewa, ba za mu iya gudanar da gagarumin atron namu, matukar ba mu samu guduanmwar da za ku iya bamu ba, domin shirya taron a acikin nasara, musamman duba da irin gudunmawar da za ku iya bayarwa,” Inji ta.
“Ba wai muna neman hukumar ta dauki nauyin mu bane, muna kawai bukatar yin hadaka da hukumar ta NPA ne , musamman duba da irin gawaurtaccen taron da muke yin yi,” A cewar shugabar.
“Fannin na bunkasa tattalin arzikin teku, abu ne da yake ci gaba da kara tumbatsa kuma abu ne, da ke da makoma mai kyau, haka fannin ne, da har yanzu, mutane ba su gama fahimtarsa ba,” Inji ta.
Ta kara da cewa, idan aka ba za daukacin bangarorin injiniyoyin zuwa rassa guda 93 da ake da su a kasar nan da kuma sauran wadanda suke a kasar waje, hakan zai kara taimaka wa, wajen kara bunkasa kasar nan.
Shugabar ta kuma bijro da batun shigar wadanda suka samu shedar kammala karatun injiniya wadanda suka samu horo daga gun kwararrun injiniyoyi suke kuma yin aiki a hukumar ta NPA.
Ta kara da cewa, bisa matakan bin ka’ida da bangaren gudanar da mulki da kungiyar ta dauka su ne, na tabbatar da duk wanda ya karaci ilimin injiniya dole ne ya kasance ya kai mataki na goma
A na sa jawabin shugaban hukumar ta NPA Dakta Abubakar Dantsoho ya sanar da cewa, kashi 70 zuwa 80 na ma’ikatan da ke aiki a hukumar ta NPA injiniyoyi ne.
Dantsoho ya kuma bai wa shugabar kungiyar tabbacin cewa, za ta yi hadaka da kungiyar ta NSE, musamman domin a kara ciyar da kasar nan gaba, inda ya buga misali da sauran kasashen duniya da suka yi hadaka da kungiyoyin injiniyoyi wanda hakan ya ba su damar samun nasara, musamam ta hanyar yin hadaka.
Shugaban ya sanar da cewa, idan aka yi hadakar da hukum
ShareTweetSendShare MASU ALAKA