FCTA ta rufe hedikwatar PDP saboda rashin biyan haraji
Published: 26th, May 2025 GMT
Hukumar Kula da Birnin Tarayya (FCTA), ta rufe hedikwatar jam’iyyar PDP da ke unguwar Wuse a Abuja.
Lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 2:05 na ranar Litinin.
Wike ya rufe ofishin FIRS da Bankin Access kan rashin biyan haraji Ana zargin wani mutum da kashe ɗan maƙwabtansa a SakkwatoJami’an FCTA sun isa ginin tare da jami’an tsaro, inda suka rufe ofishin.
Wasu ma’aikata sun nuna rashin jin daɗinsu, bayan tafka sa-in-sa na tsawo mintuna 15, jami’an FCTA sun bar ma’aikata su fitar da motoci da kayayyakinsu kafin kulle ginin.
A makon da ya gabata, FCTA ta sanar da cewa za ta ƙwace sama da kadarori 4,700 a Abuja saboda rashin biyan haraji na tsawon shekaru 10 zuwa 43.
Waɗannan kadarorin suna yankunan Central Area, Garki, Wuse, Asokoro, Maitama da Guzape.
FCTA, ta ce mallakar waɗannan filaye ya koma hannun gwamnati.
Tun daga Litinin, gwamnati ta fara ƙwace su ba tare da la’akari da wanda ya mallaki kadarar ba.
Daraktan Sashen Kula da Ci Gaban Birnin Tarayya, ya ce za a rufe waɗannan gine-gine kuma ba za a bari kowa ya shiga ba.
Ya ƙara da cewa gwamnati za ta yanke hukunci kan yadda za a yi da su a nan gaba.
Daraktan Sashen Filaye, ya bayyana cewa babu wani hukuncin kotu da ya hana FCTA ɗaukar matakin da ta ke ɗauka a yanzu, don haka za su ci gaba da yin aikinsu.
Ya kuma ce suna tantance kadarorin da suka daɗe ba su biya haraji ba daga shekara ɗaya zuwa 10, kuma za su ɗauki mataki bayan sun kammala tantancewar.
Tun a watan Maris, 2025 FCTA, ta sanar da soke takardun mallakar filaye guda 4,794 saboda rashin biyan haraji, inda ta gargaɗi cewa za ta fara karɓe ikon mallakar filayen daga ranar Litinin.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Babban Birnin Tarayya Haraji Kadarori rashin biyan haraji
এছাড়াও পড়ুন:
KEDCO ya ƙaryata asibitin AKTH kan mutuwar majinyata saboda ɗauke wuta
Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki na Shiyyar Kano (KEDCO) ya ƙaryata zargin da Asibitin Koyarwa na Aminu Kano (AKTH) ya yi masa, dangane da mutuwar wasu marasa lafiya sakamakon katse wutar lantarki da aka ce kamfanin ya yi.
Asibitin na AKTH ya bayyana damuwarsa a ranar Lahadi kan abin da ya kira abin takaici yana mai cewa mutanen da suka mutu za su iya tsira da ransu da ba a ɗauke wutar ba.
Amma a martanin da ya bayar, Shugaban Sashen Hulɗa da Jama’a na KEDCO, Sani Bala Sani, ya ce asibitin na ƙoƙarin ɓata sunan kamfanin ne kawai, domin an dawo da wutar tun kafin asibitin ya fitar da wannan sanarwar.
Sani ya bayyana cewa matsalar ta samo asali ne daga wani yunƙurin da ake yi na raba ginin asibitin da cibiyoyin lafiya daga gidajen ma’aikatan asibitin.
“Cibiyar asibitin da cibiyoyin lafiya suna da alaƙa da layin 33kV na Zariya Road wanda aka fi ba fifiko wajen raba wuta, kuma suna samun kimanin sa’o’i 22 na wutar lantarki a kullum ƙarƙashin tsarin Band A.
“Amma, shugabannin AKTH sun dage cewa sai gidajen ma’aikata sun ci gaba da kasancewa a layin wutar lantarki ɗaya da cibiyoyin lafiya. Wannan ya janyo barazana ga inganci da kwanciyar hankali na wutar da aka ware wa asibitin.
“An yi ƙoƙari sau da dama don raba gidajen ma’aikata daga cibiyoyin lafiya, amma haƙarmu ba ta kai ga cimma ruwa ba saboda ƙin amincewar shugabannin asibitin. Abin takaici, wannan ya haifar da matsala mai tsanani da ta janyo katsewar wutar da muke ƙoƙarin kaucewa,” in ji KEDCO.
Don tabbatar da wutar lantarki ba tare da katsewa ba ga asibitin, kamfanin KEDCO ya ce yana ci gaba da aikin raba layukan wutar lantarkin biyu. Ya ce annan mataki ya zama dole don tabbatar da inganci, tsaro da kyautata lantarki ga asibitin.
Kamfanin ya kuma zargi asibitin da rashin biyan kuɗin wutar lantarki da gidajen ma’aikata ke amfani da ita, wanda ke shafar ingancin ayyukan samar da wuta na kamfanin.
KEDCO ya ce a cikin wata wasiƙa da ya aike ranar 12 ga Agusta, 2025, Babban Jami’in Kasuwanci na kamfanin, Muhammad Aminu Ɗantata, ya sanar da Shugaban Asibitin AKTH game da shirin dakatar da samar da wutar lantarki ga gidajen ma’aikata da wuraren da ba su da muhimmanci, sakamakon rashin cikakken biyan kuɗin wutar wata-wata.
Wasiƙar ta bayyana cewa:
“Duk da roƙon da aka yi sau da dama, asibitin ya ƙi biyan cikakken kuɗin wutar da yake sha a duk wata.
Wannan ya haifar da bashin wutar lantarki da ya kai ₦949,880,922.45 a watan Agustan 2025.
“An bukaci asibitin ya biya kuɗin watan Agusta 2025 na ₦108,957,582.29 gaba ɗaya cikin kwanakin aiki 10, don kaucewa yanke wuta a wuraren da abin ya shafa,” in ji wasiƙar.
Kamfanin ya ƙuduri aniyar ci gaba da samar da wutar lantarki ba tare da katsewa ba ga AKTH a matsayin babbar cibiyar lafiya.
A ƙarshe, KEDCO ya roƙi shugabannin asibitin da su ba da haɗin kai a aikin raba layukan wutar, wanda ya ce yana da amfani ga marasa lafiya, ma’aikata, da al’umma baki ɗaya.