Aminiya:
2025-05-27@18:14:26 GMT

FCTA ta rufe hedikwatar PDP saboda rashin biyan haraji

Published: 26th, May 2025 GMT

Hukumar Kula da Birnin Tarayya (FCTA), ta rufe hedikwatar jam’iyyar PDP da ke unguwar Wuse a Abuja.

Lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 2:05 na ranar Litinin.

Wike ya rufe ofishin FIRS da Bankin Access kan rashin biyan haraji Ana zargin wani mutum da kashe ɗan maƙwabtansa a Sakkwato

Jami’an FCTA sun isa ginin tare da jami’an tsaro, inda suka rufe ofishin.

Wasu ma’aikata sun nuna rashin jin daɗinsu, bayan tafka sa-in-sa na tsawo mintuna 15, jami’an FCTA sun bar ma’aikata su fitar da motoci da kayayyakinsu kafin kulle ginin.

A makon da ya gabata, FCTA ta sanar da cewa za ta ƙwace sama da kadarori 4,700 a Abuja saboda rashin biyan haraji na tsawon shekaru 10 zuwa 43.

Waɗannan kadarorin suna yankunan Central Area, Garki, Wuse, Asokoro, Maitama da Guzape.

FCTA, ta ce mallakar waɗannan filaye ya koma hannun gwamnati.

Tun daga Litinin, gwamnati ta fara ƙwace su ba tare da la’akari da wanda ya mallaki kadarar ba.

Daraktan Sashen Kula da Ci Gaban Birnin Tarayya, ya ce za a rufe waɗannan gine-gine kuma ba za a bari kowa ya shiga ba.

Ya ƙara da cewa gwamnati za ta yanke hukunci kan yadda za a yi da su a nan gaba.

Daraktan Sashen Filaye, ya bayyana cewa babu wani hukuncin kotu da ya hana FCTA ɗaukar matakin da ta ke ɗauka a yanzu, don haka za su ci gaba da yin aikinsu.

Ya kuma ce suna tantance kadarorin da suka daɗe ba su biya haraji ba daga shekara ɗaya zuwa 10, kuma za su ɗauki mataki bayan sun kammala tantancewar.

Tun a watan Maris, 2025 FCTA, ta sanar da soke takardun mallakar filaye guda 4,794 saboda rashin biyan haraji, inda ta gargaɗi cewa za ta fara karɓe ikon mallakar filayen daga ranar Litinin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Babban Birnin Tarayya Haraji Kadarori rashin biyan haraji

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnati Ta Kammala Samar Da Fasfo Sama Da 200,000 Da Suka Yi Jinkiri

Kan batun gyaran gidajen yari kuwa, ministan ya nuna damuwa kan halin da gidan gyaran hali ke ciki, inda ya bayyana cewa fiye da fursunoni 4,000 na tsare ne saboda gazawarsu na biyan tara kamar Naira 50,000.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnati Ta Kammala Samar Da Fasfo Sama Da 200,000 Da Suka Yi Jinkiri
  • FCTA Ta Rufe Hedikwatar PDP Ta Ƙasa Saboda Ƙin Biyan Harajin Ƙasa
  • Wike ya rufe ofishin FIRS da Bankin Access kan rashin biyan haraji
  • Shugaban Shirin  HKI Da Amurkan  Na Raba Kayan Agaji A Gaza Ya Yi Murabus
  • Gwamnatin Gombe za ta taimaki ’yar shekara 14 da aka yi wa auren dole
  • Fiye Da Mata 300 Ne Cikinsu Ya Zube Saboda  Rashin Abinci Mai Gina Jiki A Gaza
  • Afirka Ta Kudu Ta Zargi Shugaban Kasar Amurka Da  Rashin Dalili Akan Zargin Yi Wa Fararen Fatar Kasar Kisan Kiyashi
  • Yara Miliyan 2.9 A Nijeriya Ke Fama Da Rashin Abinci Mai Gina Jiki – UNICEF
  • Rashin abinci mai gina jiki a Gaza ya yi sanadiyar mutuwar mutane 299