An bukaci Maniyyatan Jihar Jigawa su yi addu’o’i ga jihar da kasa Najeriya domin samun zaman lafiya a yayin zaman su a kasa Mai tsarki.

 

Amirul Hajj na Jihar, Mai Martaba Sarkin Kazaure Dr Najib Hussaini Adamu yayi wannan kiran a lokacin da yake jawabi ga Maniyyatan Jihar a Kasar Saudi Arabia.

 

Amirul hajjin ya hori Maniyyatan da suyi addu’a tare da karkatar da zukatansu ga dabi’u nagari, inda ya bayyana cewar canza dabi’u tare da komawa ga Allah ne kadai hanyar da za’a bi don magance matsalolin da suka addabi kasa Najeriya.

 

Dr Najib Hussaini Adamu, yace Allah ya albarkaci Jihar Jigawa da ni’imomi da dama, a don haka ya bukace su da su kara karfafa addu’o’i.

 

Kazalika, Sarkin ya kuma yabawa tallafin da gwamnati jihar ta bayar domin tabbatuwar aiwatar da hajjin bana.

 

A don haka, yayi kira ga Maniyyatan da su yi wa gwamnatin Jihar jigawan addu’a.

 

Ya kuma bukace su da su zama masu bin dokokin kasar saudiyya, yana mai horan su da su zamo masu tsafta kuma  jakadu nagari a ko ina musamman a zaman Muna.

 

Mai Martaba ya kuma kara jan hankulansu da su zama abin misali a wajen kula da tsaftar muhalli yana mai fatan Allah yasa ayi ibada lafiya a koma gida lafiya.

 

Usman Mohammad Zaria

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Rashin Tsaro: Gwamnatin Kogi Ta Gargadi Siyasantar Da Kalubalen Tsaro A Jihar

LEADERSHIP ta tuna cewa, gwamnatin jihar da jami’an tsaro sun fuskanci matsin lamba daga mazauna yankunan da lamarin ya shafa domin shawo kan lamarin.

 

Fanwo, ya ba da tabbacin cewa, gwamnati ta yi shiru, amma tana samun nasara a yakin da take da masu aikata laifuka ta karkashin kasa, musamman masu garkuwa da mutane a jihar.

 

Ya ce, nasarar da gwamnati ta samu ya biyo bayan ingantattun tsare-tsare da zurfafa hadin gwiwar hukumomin tsaro da nufin tabbatar da tsaro da walwalar kowane dan jihar Kogi.

 

Yayin da take jajantawa iyalan wadanda hare-haren na baya-bayan nan ya shafa, gwamnatin jihar ta jaddada cewa, bai kamata a yi amfani da irin wadannan kalubalen wajen yada labaran karya ko firgita jama’a ba.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • DAGA LARABA: Dalilan Rashin Jituwa Tsakanin Marasa Lafiya Da Jami’an Kiwon Lafiya
  • Rashin Tsaro: Gwamnatin Kogi Ta Gargadi Siyasantar Da Kalubalen Tsaro A Jihar
  • Kyakkyawar Hulda Tsakanin Sin Da Koriya Ta Kudu Na Da Muhimmanci Ga Zaman Lafiya Da Ci Gaban Yankinsu
  • Jami’in Makamashin Nukiyar Iran Ya Ce; Zarge-Zargen Da Ake Yi Kan Shirin Makmashin Nukiliyar Iran Siyasa Ce Kawai
  • Al’ummomi Daga Sassan Duniya Suna Yin Tofin Allah Tsine Kan Sace Masu Fafatuka A Kan Hanyarsu Ta Zuwa Gaza 
  • Ministan Harkokin Kiwon Lafiya Na Iran Ya Bukaci A Yawaita Sayar Da Kayakin Likita Zuwa Kasashen Waje
  • Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Ya Bukaci A Yawaita Sayar Da Kayakin Likita Zuwa Kasashen Waje
  • Iran ta ce a shirye take ta shiga tsakani a kokarin samar da zaman lafiya tsakanin Pakistan da Indiya
  • Sin Na Kokarin Gina Yanayin Zaman Lafiya Da Hadin Gwiwa Da Kawance A Tekun Kudancin Kasar
  • Sallah: Gwamnatin Sakkwato ta bai wa kowane Alhaji kyautar N450,000