An bukaci Maniyyatan Jihar Jigawa su yi addu’o’i ga jihar da kasa Najeriya domin samun zaman lafiya a yayin zaman su a kasa Mai tsarki.

 

Amirul Hajj na Jihar, Mai Martaba Sarkin Kazaure Dr Najib Hussaini Adamu yayi wannan kiran a lokacin da yake jawabi ga Maniyyatan Jihar a Kasar Saudi Arabia.

 

Amirul hajjin ya hori Maniyyatan da suyi addu’a tare da karkatar da zukatansu ga dabi’u nagari, inda ya bayyana cewar canza dabi’u tare da komawa ga Allah ne kadai hanyar da za’a bi don magance matsalolin da suka addabi kasa Najeriya.

 

Dr Najib Hussaini Adamu, yace Allah ya albarkaci Jihar Jigawa da ni’imomi da dama, a don haka ya bukace su da su kara karfafa addu’o’i.

 

Kazalika, Sarkin ya kuma yabawa tallafin da gwamnati jihar ta bayar domin tabbatuwar aiwatar da hajjin bana.

 

A don haka, yayi kira ga Maniyyatan da su yi wa gwamnatin Jihar jigawan addu’a.

 

Ya kuma bukace su da su zama masu bin dokokin kasar saudiyya, yana mai horan su da su zamo masu tsafta kuma  jakadu nagari a ko ina musamman a zaman Muna.

 

Mai Martaba ya kuma kara jan hankulansu da su zama abin misali a wajen kula da tsaftar muhalli yana mai fatan Allah yasa ayi ibada lafiya a koma gida lafiya.

 

Usman Mohammad Zaria

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Xi Jinping Ya Halarci Kwarya-Kwaryan Taron Shugabannin APEC Na 32 Tare Da Gabatar Da Jawabi

 

Shugaba Xi ya kuma bayyana cewa, cikakken zama na 4 na kwamiti na 20 na JKS ya amince da shirin raya kasa na shekaru biyar-biyar karo na 15. Sin za ta yi amfani da wannan damar don ci gaba da gyare-gyaren tattalin arzikinta, da kuma fadada bude kasuwancinta mai zurfi ga ketare, ta haka za ta ci gaba da ba da sabbin damammaki ga yankin Asiya da Pasifik da sauran kasashen duniya ta hanyar zamanantar da al’ummarta. (Amina Xu)

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Kirkire-kirkire Da Bude Kofa Da Raba Damar Samun Ci Gaba A Colombo October 30, 2025 Daga Birnin Sin Sin Ta Fitar Da Jerin Sakamakon Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Tawagar Kasar Da Ta Amurka Suka Cimma  October 30, 2025 Daga Birnin Sin Babban Daraktan Sakatariyar APEC: Sin Tana Ba Da Gudummawar Ba Da Jagoranci A APEC October 30, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Allah Ya yi wa Malam Nata’ala rasuwa
  • Gidauniyar IRM Da KADCHMA, Ta Ƙaddamar Da Inshorar Lafiya Kyauta Ga Mutane 200 A Kaduna
  • Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Gina Gidaje 52 A Babban Birnin Jihar
  • Zaben 2027 Zai Kasance Ne Tsakanin Mulkin Tinubu Da Zabin Ƴan Nijeriya —Atiku Abubakar
  • Gwamnatin Yobe ta ƙaddamar da shirin amfani da ma’adanai
  • Masar da Eritrea Sun Tattauna Bukatar Tallafawa Kasar Sudan
  • Kifewar Kwalekwale: Gwamnan Gombe Ya Jajanta Wa Al’ummar Nafada Kan Mutuwar Matasa Biyar
  • Xi Jinping Ya Halarci Kwarya-Kwaryan Taron Shugabannin APEC Na 32 Tare Da Gabatar Da Jawabi
  • NAJERIYA A YAU: Dalilan Da Daliban Makarantar Kudi Suka Fi Na Gwamnati Kokari