Shugaban Amurka Ya Ce: Kasarsa Da Iran Suna Kyakkyawar Tattaunnawa A Tsakaninsu
Published: 29th, May 2025 GMT
Shugaban kasar Amurka Donald Trump ya bayyana cewa: Suna gudanar da kyakkyawar tattaunawa da Iran
Shugaban Amurka Donald Trump ya bayyana cewa: Amurka na tattaunawa da Iran sosai kan Shirin makamashin nukiliyarta.
Donald Trump ya fada a ranar Laraba cewa: “Ya damu da abin da ke faruwa a Ukraine, kuma bai sani ba ko Putin na son kawo karshen yakin,” a cewar gidan talabijin na Al Jazeera.
Dangane da tattaunawar da aka yi da Iran, Trump ya ce: “Suna tattaunawa mai kyau da Iran.”
Trump ya ce: Dole ne bangarorin Gaza su amince da takardar da Steve Witkoff wakilin Amurka na musamman a yankin Gabas ta Tsakiya ya gabatar.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamna Namadi Ya Jinjinawa Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Bisa Ayyukan Raya Kasa
Gwamnatin Jihar Jigawa ta nuna matukar gamsuwa tare da yabawa Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu, Dr Builder Muhammad Uba bisa kokarin sa na ayyukan raya kasa.
Gwamna Umar Namadi ya bayyana hakan ne a lokacin kaddamar da bude ofishin shugaban karamar hukumar da kuma dakin taro na karamar hukumar da aka gudanar a sakatariyar karamar hukumar ta Birnin Kudu.
Ya ce shugaban karamar hukuma, Dr Builder Muhammad Uba mutum ne mai kwazo da himma wanda ya zamto abin koyi a bangaren shugabanci.
A don haka, Malam Umar Namadi ya yi kira ga sauran shugabanin kananan hukumomin jihar da su tashi tsaye wajen gudanar da ayyukan kyautata rayuwar al’ummar su domin sharbar romon mulkin dimokradiyya.
A jawabinsa na godiya shugaban ƙaramar hukumar, Dr Builder Muhammad Uba ya godewa Gwamnan bisa samun damar bude ofishin da kuma dakin taro na karamar hukumar.
Wakilinmu ya ba mu rahoton cewar, Gwamnan ya sami rakiyar Mataimakinsa, Injiniya Aminu Usman Gumel da Shugaban Majalisar Dokokin Jihar, Alhaji Haruna Aliyu Dangyatun da Sakataren Gwamnati Alhaji Bala Ibrahim da Shugaban Jami’yya na Jihar Alhaji Aminu Sani Gumel da Kwamishinoni da sauran mukarraban gwamnatin jihar.
Usman Mohammed Zaria