Da yake jawabi ga ɗimbin mutanen da suka halarci wannan tattaki, Gwamna Lawal ya jaddada ƙudirin gwamnatinsa na kawar da duk wani nau’in miyagun laifuka a jihar, tare da mai da hankali sosai kan ‘yan bindiga.

Ya ce, “A yau mun fito dubunnan mu domin mu yi tattakin samun zaman lafiya, domin mu sanar da duniya cewa Zamfara ta samu ci gaba sosai ta fuskar tsaro.

“Gwamnatina ta ba da himma da kayan aiki masu yawa don ƙarfafa sojoji, tattara bayanan sirri, da haɗa kai don dawo da zaman lafiya a jihar.

“Mun sami gagarumar nasara a yaƙin da ake yi da ‘yan bindiga, yawancin wuraren da ake fama da rikici a baya, a halin yanzu sun kasance cikin kwanciyar hankali. Hanyoyin da a da ba a iya wucewa, a yanzu matafiya na wucewa lami lafiya cikin ‘yanci.

 

“Kuna iya ganin yadda mutane ke tafiya cikin walwala tare da gudanar da ayyukansu na yau da kullum da kuma yadda suke taruwa cikin farin ciki don yin tattakin samar da zaman lafiya. Wannan ya nuna a fili cewa mutanenmu sun samu zaman lafiya kuma suna son zaman lafiya. Hakan kuma ya nuna cewa jama’a sun fahimta kuma sun yaba da abin da gwamnatin jihar ke yi don inganta zaman lafiya.”

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: zaman lafiya

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Ayukka 16 A Sakkwato

A wani babban ci gaba na kawo sauyi a tsarin kiwon lafiyar Najeriya, gwamnatin tarayya ta yi  ta kaddamar da ayyuka 16 a asibitin masu tabin hankali na gwamnatin tarayya dake Kware a jihar Sokoto.

 

Da yake jawabi a wajen bikin kaddamarwar, Ministan Kasa a ma’aikatar Lafiya da walwalar jama’a, Dokta Iziak Salako, ya jaddada cewa ayyukan na daga cikin ajandar sabuwar fata ta gwamnati shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu na karfafa cibiyoyin kiwon lafiya na kasa.

 

Ya ce FG ta himmatu wajen samar wa asibitoci kayayyakin more rayuwa, kayan aiki da kudade, da tallafi don inganta ayyukan hidima a fadin kasar.

 

Dakta Salako ya ci gaba da bayyana cewa, gwamnatin tarayya ta samar da muhimman ayyuka sama da 500 na samar da ababen more rayuwa tare da samar da ingantattun kayan aikin jinya ga manyan cibiyoyin kiwon lafiya a fadin kasar nan.

 

Ministan ya kuma bayyana cewa FG ta dauki ma’aikatan lafiya sama da 15,000 aiki a karkashin shirin bunkasa sana’o’in da ake yi.

 

Dokta Salako ya ce ma’aikatar lafiya ta fara aiwatar da dokar kula da lafiyar kwakwalwa ta Najeriya, 2023, da nufin samar da cikakken sashen kula da lafiyar kwakwalwa a wani yunkuri na hada ayyukan kula da lafiyar kwakwalwa cikin harkokin kiwon lafiya na farko a fadin kasar nan.

 

Rediyon Najeriya da ke Sokoto ya rawaito cewa sabbin ayyukan da aka kaddamar sun hada da dakin gwaje-gwaje na Molecular, Sashen Kula da Lafiyar Jama’a, ICU, Cibiyar Kula da Dogaro da Magungunan Mata da Yara na Yanki, Cibiyar Ba da Agajin Gaggawa, Dakunan kwanan dalibai da yawa, Makarantar Koyon kula da masu tabin hankali, ICT da dai sauransu.

 

Shima da yake nasa jawabin, kwamishinan lafiya na jihar Sokoto, Dakta Faruku Wurno, ya nanata kudurin jihar na yin hadin gwiwa da asibitin ta Kware, inda ya bayyana yadda tsarin kula da lafiya na asibitin zai karfafa hadin gwiwa da bayar da hidima.

 

Dokta Wurno ya yabawa Daraktan kula da lafiya na asibitin Farfesa Shehu Sale bisa jajircewarsa da ya yi, ya kuma bukaci wadanda suka gaje shi da su kara azama kan taswirar ci gaban da aka riga aka shimfida.

 

NASIR MALALI

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Bayan Biyan Basussuka: WAEC Da NECO Sun Saki Samakon Jarrabawar Jihar Zamfara
  • Gwamnatin Jihar Gombe Ta Rattaba Hannu Kan Yarjejeniya Domin Gina Mayankar Dabbobi
  • Save The Children Ta Shirya Taron Bita Ga Yan Jarida Da Kungiyoyi Masu Zaman Kansu A Kaduna.
  • Shekaru 6: Don amfanin matasa mun inganta ilimi da noma — Gwamna Buni 
  • Shekaru 6: Don amfanin matasa mun inganta harkokin ilimi, noma — Gwamna Buni 
  • An gano gawar direba a cikin mota a Bayelsa
  • Majalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince Da Dokokin Ilimin Noma da Gyaran Kotunan Gargajiya
  • MDD Ta Gudanar Da Bikin Ranar Tunawa Da Dakarun Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Duniya Ta 2025
  • Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Ayukka 16 A Sakkwato