Hana shigar da abinci da Isra’ila ta yi zuwa Gaza ‘laifi ne na yaki’: MDD
Published: 31st, May 2025 GMT
Jami’in kula da ayyukan jin kai na Majalisar Dinkin Duniya ya ce matakin da Isra’ila ta dauka na hana agajin abinci ga Falasdinawa da ke fama da yunwa a yankin Zirin Gaza da aka yi wa kawanya ya zama laifin yaki.
“Muna ganin abinci dake jibge a kan iyakoki kuma ba a ba da izinin shigar da shi ba a lokacin da jama’a a gefen iyakar ke fama da yunwa, a yayin da muke jin ministocin Isra’ila suna cewa sun ayin hakan ne don matsa lamba kan al’ummar Gaza,” in ji Mataimakin Sakatare Janar na Majalisar Dinkin Duniya Tom Fletcher a wata hira a ranar Jumma’a.
Irin wannan na a matsayin laifin yaki ne,” in ji shi.
Baya ga hakan ma a cikin ‘yan kwanakin nan, sojojin Isra’ila sun kashe masu neman agaji da dama a lokacin da suke kokarin isa wurin rarraba kayan agaji a yammacin Rafah a karkashin tsarin Amurka da Isra’ila.
Tuni dai hukumomin agaji na kasa da kasa suka yi gargadin cewa shirin da Isra’ila ke yi na sarrafa rabon kayan agaji a zirin Gaza, ciki har da shawarar da Amurka ke marawa baya, zai kara wahalhalu a yankin Falasdinawa.
A baya-bayan nan ne dai shugaban hukumar kula da ‘yan gudun hijira ta Majalisar Dinkin Duniya (UNRWA) ya yi Allah-wadai da sabon salon agajin da Amurka ke marawa baya a Gaza, yana mai cewa “wani cin zarafi” da ke faruwa a can.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: da Isra ila
এছাড়াও পড়ুন:
Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Aiwatar Da Kisan Kiyashi Kan Falasdinawa A Yankin Zirin Gaza
A tsawon kwanaki 602 a jere, sojojin mamayar Isra’ila suna ci gaba da aiwatar da kisan kiyashi kan Falasdinawa a yankin Zirin Gaza
Sojojin mamayar Isra’ila na ci gaba da yakin da suke yi na kisan kiyashi a zirin Gaza, inda suka sake kaddamar da wani sabon yaki kan Gaza bayan tsagaita bude wuta. Hakan ya biyo bayan sauya ra’ayi da Fira ministan gwamnatin haramtaciyar kasar Isra’ila Benjamin Netanyahu ya yi kan yarjejeniyar tsagaita bude wuta, bisa la’akari da goyon bayan siyasa da na soji da Amurka ke ba shi, a cikin shiru da kasashen duniya suka yi da kuma gazawar da ba a taba gani ba daga kungiyoyin kasa da kasa.
Kafofin yada labaran Falasdinu sun ruwaito cewa: Sojojin mamayar Isra’ila sun kaddamar da jerin hare-hare ta sama kan yankunan Gaza, da nufin tsaurara tasirin hana shigar da kayan abinci da ya karu tun farkon watan Maris. Wannan ya ba da mummunan hoto na yunwar da mazauna Gaza ke fuskanta.
A safiyar yau Juma’a, jiragen saman yakin gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila suka kaddamar da wani mummunan farmaki kan yankunan kudancin Khan Yunus. Kamar yadda sojojin na Isra’ila suka yi luguden wuta kan sansanin ‘yan gudun hijira na Al-Bureij da ke arewacin zirin Gaza da kuma arewa maso yammacin Rafah.