Ma’aikatar kudi ta kasar Sin ta ce kamfanoni mallakin gwamnatin kasar, sun gudanar da ayyukansu yadda ya kamata cikin watanni hudu na farkon shekarar nan ta 2025, inda jimillar kudaden shigarsu ta ci gaba da karuwa bisa daidaito a shekara guda.

Alkaluman da ma’aikatar ta fitar a Larabar nan, sun nuna tsakanin watan Janairu zuwa Afirilu, jimillar kudaden gudanarwa na wadannan kamfanoni ya kai kudin Sin yuan tiriliyan 26.

276, kwatankwacin dalar Amurka tiriliyan 3.65, adadin da ya nuna daidaito matuka idan an kwatanta da na makamancin lokaci na shekarar 2024. (Mai fassara: Saminu Alhassan)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Yadda kotu ta yanke wa wanda ya kona mutane a cikin masallaci hukuncin rataya a Kano

Babbar Kotun Musulunci a Jihar Kano ta yanke wa Shafiu Abubakar hukuncin kisa ta hanyar rataya saboda cinna wuta a wani masallaci a kauyen Gadan, Karamar Hukumar Gezawa, yayin da jama’a ke tsaka da jam’in sallar asuba a ranar 15 ga Mayu, 2024. Harin ya yi sanadiyar mutuwar mutane 23 tare da raunana wasu.

An samu Shafi’u da laifuka hudu, ciki har da kisan kai da kuma barna ta hanyar gobara. Baya ga hukuncin kisa, alkali ya ba da umarnin a yi masa bulala 150, tare da biya tarar N1,500, sannan kuma a kwace babur dinsa mai kafa uku, inda za a sayar, a yi amfani da kudin da aka samu wajen gyaran masallacin da ya lalace.

Yayin shari’ar, masu gabatar da kara sun gabatar da shaidu bakwai, ciki har da hakimin kauye da kuma wani jami’in ’yan sanda.

Daya daga cikin shaidun, wanda dan uwan Shafi’u ne, ya bayyana cewa wanda ake tuhumar yana da tarihin kokarin cutar da ’yan uwa, kuma an bayyana shi a matsayin mai cikakken hankali bayan binciken tabin hankali.

An yanke wa wanda ya yi wa agolarsa fyaɗe ɗaurin rai-da-rai  Jama’ar gari sun kashe DPO, sun ƙona ofishin ’yan sanda a Kano 

Wani shaida kuma ya bayyana yadda ya tsira a lokacin da masallacin da ke ci da wuta tare da munanan raunuka kuma ya ga Shafi’u yana gudu.

Shafiu ya shaida wa kotun cewa ya sayi man fetur a ranar 14 ga Mayu, 2024, don yayyafa wa masallacin sannan ya cinna masa wuta, ya rufe kofofinsa kuma ya samu konewa a lokacin da yake aikata laifin. Furucinsa, tare da konewar da ke bayyane a hannayensa yayin bayyanarsa a kotu, sun tabbatar da shari’ar masu gabatar da kara.

Daraktan gabatar da kara na Jihar Kano ya bayyana gamsuwarsa da hukuncin, inda ya bayyana cewa ya nuna girman laifin.

Sai dai lauyan Shafi’u ya nuna yiwuwar daukaka kara tare da nuna damuwa game da yanayin da yake tsare.

An ruwaito cewa lamarin ya samo asali ne daga rikicin gado, inda Shafi’u ya yi niyyar kai hari ga ’yan uwansa da ya yi imanin sun zalunce shi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • NAHCON ta kammala jigilar maniyyata aikin hajjin 2025
  • Atiku Ya Caccaki Gwamnatin Tinubu, Ya Yi Gargaɗi Kan Cin Sabon Bashi
  • Ko kwabo ban ciyo bashi ba tun da na zama Gwamnan Kaduna – Uba Sani
  • Gwamnatin Kano Ta Yi Barazanar Hukunta Matasa Masu Janyo Rikice-Rikice
  • Sojoji Sun Koka Bisa Jinkirin Yanke wa Ƴan Ta’adda 1,450 Hukunci
  • Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Nuna Misali Na Bude Kofa Da Raya Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da ASEAN Da GCC
  • Yadda kotu ta yanke wa wanda ya kona mutane a cikin masallaci hukuncin rataya a Kano
  • Gwamnatin Kano Zata Gina Masallacin Da Aka Ƙona Masallata A Gezawa
  •  Fizishkiyan: Wajibi Ne A Kawo Karshen Ta’addanci A Kan Iyakokin Iran Da Pakistan