Falasdinwan Akalla 16 Sojojin HKI Suka Kashe A Gaza Ya Zuwa Yanzu A Yau Laraba
Published: 28th, May 2025 GMT
Majiyar kungiyoyin bada taimakon gaggawa a Gaza sun bayyana cewa ya zuwa lokacin bada wannan labarin a yau Laraba, sojojin yahudawan Sahyoniyya sun kashe akalla mutane 16.
Shafin labarai na Arab News ta kasar Saudia ya nakalto Mahmud Bassal kakakin wata kungiyar bada agaji na Gaza yana cewa da misalign karfe biyun dare jiragen yakin HKI sun kai hare-hare kan gidan Osama Al-arbeed dan jarida mai daukar hotuna a gidansa da ke arewacin Gaza, inda harin ya raunata Osman Arbeed sannan ya kashe wasu daga cikin yan gidansa.
Har’ila yau wasu mutane 6 sun kai ga shahada a yayinda wasu 15 suka ji rauni daga ciki har da yara kanana, a garin Khan Yunus a safiyar yau Laraba. A lokacin da kamfanin dillancin labaran AFP na kasar Faransa ya tuntubi sojojin HKI dangane da wadannan hare-haren basu bada amsa ba.
A cikin watan da ya gabata ne gwamnatin Natanyahu ta kara yawan hare-hare a gaza, na nufin samun abinda ya kira cikekken Nasara a kan Hamas a gaza. Don haka ne sojojin HJI suke kashe falasdinawa gwargwadon iyawarsu a Gaza a ko wace rana.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Juventus ta ɗauki tsohon kociyan Italiya, Luciano Spalleti
Kungiyar ƙwallon ƙafa ta Juventus ta naɗa Luciano Spalletti a matsayin sabon kociya bayan sallamar Igor Tudor da ta yi a farkon makon nan.
Juventus ta ƙulla yarjejeniya da tsohon kociyan na Inter Milan da Roma da Udinese da Zenit St Petersburg da kuma tawagar ƙasar Italiya, har zuwa ƙarshen wannan kakar, yayin da take fatan samu gurbin zuwa gasar Kofin Zakarun Turai ta Champions League ta baɗi.
Babu wani uzuri da za a yi wa sabbin hafsoshi kan matsalar tsaron Nijeriya — Tinubu Borno ta fara fitar da kayan robobi zuwa ƙasashen waje – ZulumSpalletti, shi ne kociyan da ya jagoranci Napoli wajen lashe gasar Serie A a 2023, wadda ita ce karon farko cikin shekaru 33, inda a yanzu ake fatan zai ƙara daidaita Juventus da ke fama da rashin katabus da matsalolin kuɗi tun daga 2022.
Spalletti, wanda aka sani da ƙwarewa wajen gina ƙungiya mai ƙarfi, ya dawo horaswa bayan gazawar da ya yi a matsayin kociyan Italiya a gasar Euro 2024, da kuma shan kashi a hannun Norway yayin wasan farko na neman tikitin Gasar Kofin Duniya ta 2026.
Zuwa yanzu dai Juventus tana matsayi na bakwai a gasar Serie A da tazarar maki shida tsakaninta da Napoli da ke saman tebur, inda wasan farko da Spalletti mai shekaru 66 zai ja ragama shi ne da Cremonese.