Majiyar kungiyoyin bada taimakon gaggawa a Gaza sun bayyana cewa ya zuwa lokacin bada wannan labarin a yau Laraba, sojojin yahudawan Sahyoniyya sun kashe akalla mutane 16.

Shafin labarai na Arab News ta kasar Saudia ya nakalto Mahmud Bassal kakakin wata kungiyar bada agaji na Gaza yana cewa da misalign karfe biyun dare jiragen yakin HKI sun kai hare-hare kan gidan Osama Al-arbeed dan jarida mai daukar hotuna a gidansa da ke arewacin Gaza, inda harin ya raunata Osman Arbeed sannan ya kashe wasu daga cikin yan gidansa.

Har’ila yau wasu mutane 6 sun kai ga shahada a yayinda wasu 15 suka ji rauni daga ciki har da yara kanana, a garin Khan Yunus a safiyar yau Laraba. A lokacin da kamfanin dillancin labaran AFP na kasar Faransa ya tuntubi sojojin HKI dangane da wadannan hare-haren basu bada amsa ba.

A cikin watan da ya gabata ne gwamnatin Natanyahu ta kara yawan hare-hare a gaza, na nufin samun abinda ya kira cikekken Nasara a kan Hamas a gaza. Don haka ne sojojin HJI suke kashe falasdinawa gwargwadon iyawarsu a Gaza a ko wace rana.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Sojoji Sun Kashe Kwamandan Boko Haram Ibn Khalid A Borno

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojoji Sun Kashe Kwamandan Boko Haram Ibn Khalid A Borno
  • Iran: Sojojin Ruwan Iran Sun Kori Jirigin Yakin Amurka Daga Tekun Oman
  • An Kama Wata Mata Da Take Shirin Kashe Benjemin Netanyahu
  • A Kalla Falasdinawa 10 Yunwa Ta Kashe A Gaza A Cikin Sa’o’i 24
  • Uwa ta kashe ’ya’yan cikinta biyu saboda kuncin rayuwa
  • Sojojin Yemen Sun Kai Hari Kan Filin Jirgin Lod Na Isra’ila Da Makami Mai Linzami Nau’in Flasdinu
  • DAGA LARABA: Abubuwan da ya kamata yara su yi yayin hutun makaranta
  • Zazzaɓin Lassa ya kashe mutum 151 a Nijeriya bana — NCDC
  • WHO Ta Buƙaci Isra’ila Ta Saki Ma’aikacinta Da Aka Kama A Gaza
  • Hukumar Kashe Gobara Ta Jihar Kwara Ta Taimaka Wajen Hana Lalacewar Wani Bene A Ilorin