HausaTv:
2025-05-27@18:58:12 GMT

Sheikh Na’im Kassim: Gwagwarmaya Tana Da Wata Hanyar Ta Korar ‘Yan Mamaya

Published: 26th, May 2025 GMT

Babban magatakardar kungiyar Hizbullah ta kasar Lebanon Sheikn Na’im Kassim ya bayyana cewa; Idan har gwamnatin kasar ta gajiya wajen yin abinda ya rataya a wuyanta na aiki da tsagaita wutar yaki, to gwgawarmaya tana da wata hanyar da za ta yi aiki da ita akan ‘yan mamaya.

Sheikh Na’im Kassim wanda ya gabatar da jawabi a jiya danage da zagayowar cikar shekaru 25 daga korar ‘yan sahayoniya daga kasar Lebanon da gwgawarmaya ta yi, ya jaddada cewa; “Gwagwarmaya ba za ta yi shiru ba, ba kuma za ta mika wuya ba, tana yin hakuri ne saboda ta bayar da Karin lokacin,don haka ya zama wajibi a yunkura.

Sheikh Na’im Kassim ya kuma ce; Gwamnati ce mai hakkin ganin an yi aiki da tsagaita wutar yaki a Lebanon, amma idan gwamnatin ta kasa, to da akwai mafita a hannun gwgawarmaya.”

Babban magatakardar kungiyar ta Hizbullah ya kuma ce; Aikin gwgawarmaya shi ne kare kai, da kuma kin mika kai ga ‘yan mamaya, wani lokaci tana yaki, wani lokacin kuma tana takawa ‘yan mamaya birki, ko ta yi hakuri tana jira amma tana cikin shiri.”

Sheikh Na’im Kassim ya kuma ce, makami ana yin amfani da shi ne bisa dacewar maslaha.”

Wani sashen na jawabin sheikh Na’im Kassim ya kunshi cewa; A wurin gwagwarmaya har yanzu yaki bai kare ba, kuma abinda Isra’ila take yi, yana karawa gwgawarmaya karfi ne da tsayin daka.”

Haka nan kuma ya ce; Kamar yadda babu wanda ya isa ya kawar da Lebanon, babu wanda kuma zai iya kawar da gwagwarmaya daga Lebanon.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: Na im Kassim ya

এছাড়াও পড়ুন:

‘Yan Bindiga Sun Kashe Jami’an Tsaro 5 A Katsina

Jami’an da aka kashen da suka hada da Kwamandan CWC Mallam Sanusi, rahotanni sun bayyana cewa, suna cikin wani aikin kai dauki ne yayin da wasu ‘yan bindiga kusan ashirin (20) dauke da makamai a babura suka yi musu kwanton bauna a madatsar wani rafi.

 

A cewar wata sanarwa da babban sakataren yada labarai na gwamnan, Ibrahim Kaula ya fitar, maharan wadanda suka boye jikin bishiyar mangwaro, sun kona motar jami’an tsaro kirar Hilux a yayin harin.

 

 

Gwamna Radda ya samu rakiyar kwamishinan tsaro na cikin gida da harkokin cikin gida, Dr. Nasiru Danmusa; Kwamishinan ’Yansandan Jihar, Daraktan Ma’aikata na Jihar, Shugaban Ma’aikata, Alhaji Abdulkadir Mamman Nasir; da sauran manyan jami’an tsaro.

 

Shugaban karamar hukumar, Alhaji Shamsudeen Sayaya ne ya jagoranci Radda zuwa inda harin ya faru.

 

Yayin da yake jawabi ga manema labarai yayin ziyarar, Gwamna Radda ya yi Allah-wadai da harin, yana mai bayyana shi a matsayin “rashin rashi ga jihar,” sannan ya sha alwashin cewa gwamnatinsa za ta kara kaimi wajen tabbatar da tsaron dukkan al’umma.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Ta Jaddada Cewa: Ba Zata Taba Amincewa Da Batun Dakatar Da Sarrafa Uranium Ba
  • Wani abu ya fashe kusa da barikin soji a Abuja
  • Shugaban Jam’iyyar Adawa A Burtaniya Ya Ce HKI Tana Yaki A Gaza Ne A Madadin Gwamnatin Kasar
  • Iran Tana Gudanar Da Ayyukan Cibiyoyin Makamashin Nukiliyarta Bisa Maslahar Kasarta Ne
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Jami’an Tsaro 5 A Katsina
  • Ministan Gine-Ginen Hanyoyi Na Kasar Iran Tana Kasar Iraki Don Kula Da Aikin Layin Dogo
  • An Gudanar da Zabukan Larduna A Kudancin Kasar Lebanin A Cikin Barazanar HKI
  • An Gargadi Shugaban Amurka Dangane Da Fadawa Iran Da Yaki
  • Firaministan Sin Ya Sauka A Indonesia Domin Ziyarar Aiki