Jama’ar gari sun kashe DPO, sun ƙona ofishin ’yan sanda a Kano
Published: 27th, May 2025 GMT
Mutanen garin Rano ake Jihar Kano sun kashe DPO na Babban Ofishin ’Yan Sandan garin tare da banka wa ofishin wuta
Fitattun jama’ar gari sun kai wa Hedikwatar ’Yan Sanda da ke Rabin hari ne a sakamakon mutuwar matashin a hannun ’yan sandan.
Wasu sanarwar da kakakin rundunar ’yan sanda a Jihar Kano, S.
Ya bayyana cewa an kama matashin ne bisa laifin tuka babur ba cikin danganci kuma zargin yana yin haka ne bayan shaye-shayen ƙwayoyi.
NAJERIYA A YAU: Matsalolin Da Suke Tarnaki Ga Kananan Yara A Najeriya Da Hanyoyin Magance Su Wani abu ya fashe kusa da barikin soji a AbujaSanarwar ta bayyana cewa, wanda aka kama din wani makaniken babur ne wanda korafe-korafen jama’a suka yi yaw a kansa.
Ya ce, a yayin da yake tsare, ya nuna alamun rashin lafiya inda aka kai shi babban asibitin Rano, inda ya mutu da safiyar ranar 26 ga Mayu, 2025, da misalin karfe 6:00 na safe.
A sakamakon gaka, wasu gungun fusatattun mutane suka dkai hari a hedikwatar ’yan sanda ta Rano, inda suka cinna wuta a wasu sassan ofishin, suka lalata motoci goma, sannan suka kona wasu biyu.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Sanda jama ar gari ƙona ofishin yan sanda Rano
এছাড়াও পড়ুন:
Wike ya rufe ofishin FIRS da Bankin Access kan rashin biyan haraji
Hukumar Kula da Babban Birnin (FCTA) Tarayya ta rufe ofishin Hukumar Tara Haraji ta Kasa (FIRS) da kuma ginin Bankin Access kan rashin biyan haraji na sama da shekaru 25.
Daraktan Kula da Filaye na Hukumar FCTA, Chijioke Nwankwoeze, ya bayyana cewa hukumar bin ginin da bankin Access yake bashin harajin shekara 35, ofishin FIRS da ke unguwar Wuse Zone 5 kuma bashin harajin shekara 25.
Babban Ofishin na FIRS na daga cikin fitattun gine-gine da Hukumar Tara Kuɗaɗen Haraji na Babban Birnin ta rufe a safiyar Litinin, kan zargin rashin biyan haraji.
Sauran sun shafa da ginin Bankin Access da da ofishin kamfanin mai Total Energy da fitaccen otel din Ibro Hotel a unguwar Wuse, da sauran wurare 4,700 a Abuja.
Rikici ya barke a taron Atiku da kungiyoyin Arewa NAJERIYA A YAU: Tasirin Dangantakar Bangaren Zartarwa Da Na Majalisa A Kan TalakaChijioke Nwankwoeze, ya bayyana cewa ginin bankin Access da matakin ya shafa, mallakin wani wani kamfani ne, inda bankin ta kama haya.
Kazalika hukumar ta kwace izinin mallakar wasu filaye a wasu fitattun unguwanni saboda matsalar rashin biyar harajin.
Daraktan Kula da Bunƙasa Birnin Abuja, Mukhtar Galadima, ya jagoranci aikin ne bayan hukumar ta fitar da sanarwar rashin biyan harajin da ya kamata.
Ya bayyana cewa ana bin kamfanin Total harajin Shekara 10, wanda ya cika a watan Maris na 2025.
Fili mai lamba 2456 da ke titin Cadastral Zone A02, a unguwar Maitama, mallakin Kamfanin Rana Taher Furniture saboda rashin biyan harajin kas ana shekara 34.
Galadima ya bayyana cewa aikin zai ci gaba a sauran unguwannin Abuja, yana mai gargaɗin waɗanda abin ya shafa su gaggauta yin abin da aya kamata, ko su kuka da kansu.
Hukumar FCDA ta tsaurara matakan karbar haraji, musamman kam dokokin da suka shafi gine-gine da mallakar kasa a ƙarƙashin Minista mai ci, Barista Nyesom Wike.
Ya bayyana cewa wajibi ne masu filayen da hukumar ta kwace su tashi nan take, su bi hanyar da ta dace domin warware duk wata matsala.