Gaza : Spain ta bukaci kasashen duniya su kakabawa Isra’ila takunkumi
Published: 26th, May 2025 GMT
Kasar Spain ta bukaci kasashen duniya dasu kakabawa Isra’ila taklunkumi saboda ci gaba da yin fatali da kiraye-kirayen da ake matana tadakatar da yakin da take a Gaza.
Ministan harkokin wajen Spain José Manuel Albares ya ce kamata ya yi kasashen duniya su kakabawa Isra’ila takunkumi domin kawo karshen munanan hare-haren soji a zirin Gaza da aka yi wa kawanya.
Shugaban diflomasiyyar Spain yana magana ne gabanin wani babban taron kasashen Turai da na Larabawa da za a yi ranar Lahadi a Madrid.
“Dole ne mu komai, don kawo karshen wannan yakin,” in ji shi.
M.Albares ya bukaci a shigar da agajin jin kai, ba tare da wani sharadi ba, ba tare da tsangwama ba, ta yadda Isra’ila ba ta yanke shawarar wanda zai iya ci da wanda ba zai iya ba.
Taron na ranar Lahadi, wanda ya hada da wakilan kungiyar hadin kan kasashen Larabawa da kungiyar hadin kan kasashen musulmi, na da nufin ingiza bukatar da wasu kasashen duniya ke mikawa na samar da kasashe biyu da bufin kawo karshen rikicin da aka kwashe shekaru anayi.
Isra’ila dai na fuskantar matsin lamba daga kasashen duniya, musamman daga kawayenta na kut-da-kut kan ta dakatar da kai hare-haren da take kaiwa da kuma ba da damar kai agajin jin kai a Gaza.
A wannan makon ne Tarayyar Turai ta kada kuri’ar amincewa da sake duba yarjejeniyar kungiyar da Isra’ila.
A halin da ake ciki kuma, a baya-bayan nan kasar Sweden ta ce za ta matsa wa kungiyar mai kasashe 27 lamba kan ta kakaba takunkumi kan ministocin Isra’ila, yayin da Birtaniyya ta dakatar da tattaunawar cinikayya cikin ‘yanci da Isra’ila.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: kasashen duniya
এছাড়াও পড়ুন:
Kofin Duniya: Kasar Saudiyya Za Ta Sassauta Dokar Hana Shan Giya A Wuraren Yawon Bude Ido 600
A cewar jami’ai, za’a tsara yadda tsarin fitar da barasar zai kasance ta hanyar tabbatar da cewar an ba da horo ga masu sayar da ita da kuma basu takardar lasisin sayar da barasar. Hakazalika, za a tsaurara ka’idoji akan sayar da barasa a kasar, gwamnati ta jaddada cewa ana gabatar da sauye-sauyen ne cikin taka-tsantsan tare da kula da al’adun al’ummar kasar.
“Manufar ita ce, maraba da duniya ba tare da rasa asalin al’adu ba, sanya Saudiyya a matsayin mai ci gaba, duk da haka mai mutunta taswirar yawon shakatawa na duniya,” in ji hukumomin Saudiyya a cikin wata sanarwa.
Matakin ya zo ne a daidai lokacin da Saudiyya ke neman yin gogayya da kasashe makwabta kamar Hadaddiyar Daular Larabawa da Bahrain, inda a bisa ka’ida ake samun barasa a wuraren yawon bude ido.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp