Gaza : Spain ta bukaci kasashen duniya su kakabawa Isra’ila takunkumi
Published: 26th, May 2025 GMT
Kasar Spain ta bukaci kasashen duniya dasu kakabawa Isra’ila taklunkumi saboda ci gaba da yin fatali da kiraye-kirayen da ake matana tadakatar da yakin da take a Gaza.
Ministan harkokin wajen Spain José Manuel Albares ya ce kamata ya yi kasashen duniya su kakabawa Isra’ila takunkumi domin kawo karshen munanan hare-haren soji a zirin Gaza da aka yi wa kawanya.
Shugaban diflomasiyyar Spain yana magana ne gabanin wani babban taron kasashen Turai da na Larabawa da za a yi ranar Lahadi a Madrid.
“Dole ne mu komai, don kawo karshen wannan yakin,” in ji shi.
M.Albares ya bukaci a shigar da agajin jin kai, ba tare da wani sharadi ba, ba tare da tsangwama ba, ta yadda Isra’ila ba ta yanke shawarar wanda zai iya ci da wanda ba zai iya ba.
Taron na ranar Lahadi, wanda ya hada da wakilan kungiyar hadin kan kasashen Larabawa da kungiyar hadin kan kasashen musulmi, na da nufin ingiza bukatar da wasu kasashen duniya ke mikawa na samar da kasashe biyu da bufin kawo karshen rikicin da aka kwashe shekaru anayi.
Isra’ila dai na fuskantar matsin lamba daga kasashen duniya, musamman daga kawayenta na kut-da-kut kan ta dakatar da kai hare-haren da take kaiwa da kuma ba da damar kai agajin jin kai a Gaza.
A wannan makon ne Tarayyar Turai ta kada kuri’ar amincewa da sake duba yarjejeniyar kungiyar da Isra’ila.
A halin da ake ciki kuma, a baya-bayan nan kasar Sweden ta ce za ta matsa wa kungiyar mai kasashe 27 lamba kan ta kakaba takunkumi kan ministocin Isra’ila, yayin da Birtaniyya ta dakatar da tattaunawar cinikayya cikin ‘yanci da Isra’ila.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: kasashen duniya
এছাড়াও পড়ুন:
Hizbullah Ta Kasar Lebanon Ta Godewa JMI Dangane Da Tallafawa Kungiyar Saboda Gwagwarmaya Da HKI
Babban sakataren kungiyar Hezbullah ta kasar Lebanon Sheikh Na’em Qasim ya godewa shugabancin JMI, wato Imam Sayyif Aliyul Khaminaei kan goyon bayan da yake bawa kungiyar babu kakkautawa don yakar makiyar kasar HKI.
Shugaban kungiyar ya bayyana haka ne a lokacinda yake hira da tashar talabijin ta Al-Mayadeen ta kasar Lebanon, a karon farko tun bayan shahadr shugaban kungiyar Sayyid Hassan Nasarallah a shekarar da ta gabata.
Babban malamin ya kara da cewa, taimakon da Imam Khaminae yayiwa kungiyar Hizbullah, ya kai matsayinda ba zamu tambaya, ko roka ba. Musamman bayan fara yaki a cikin watan Octoban shekara ta 2023, kuma ta bada wadannan taimakon ba tare da ta shiga yakin kai tsaye ba.
Sheikh Qasem ya bayyana cewa, bamu bukaci JMI ta shiga yakin ba, kuma bai kamata ta shiga yakin ba, saboda muma bama bukatar da shiga yakin.
Daga karshen shugaban kungiyar ya bayyana cewa zancen da aka cika duniya da shin a cewa kungiyar ta mika makamanta ga gwamnatin kasar. Saboda takurawar da manya-manyan kasashen duniya suke yi don shi ne bukatar HKI.
Don haka yamata su san cewa bamu da Kalmar mika kai a kamusimmu, ko nasara ko shahada babu wata na uku iji shi.
Kuma wannan halin da ake ciki, na keta hurimun yarjeniyar 1701 wanda HKI take yi ba zai dore har’abada ba.