HausaTv:
2025-07-23@22:40:33 GMT

OPEC+ Ta Fara Shirin Ayyana Yawan Man Fetur Da Zata Haka Zuwa Sekara Ta 2027

Published: 29th, May 2025 GMT

Kungiyar kasashe masu arzikin man fetur da kuma kawayenta a wajen kungiyar sun gudanar da taro a birnin Riyad na kasar Saudia inda suka tattauna kan yawan man fetur da zasu haka daga shekara da ta 2027.

Shafin yada labarai na tanar gizo na kasar Saudia Arab News ya bayyana cewa wannan yana daga cikin abinda kasashe suka amince a bayan kuma a halin yanzu kungiyar ta rika ta tsara yawan man da ko wace kasa zata haka daga shekara ta 2022 har zuwa shekara ta 2026.

Labarin ya kara da cewa kungiyar tana da tsare tsaren haka man fetur har guda uku biyu suna tafiya kamar yadda suka tsara a yayinda daya kuma sun warewa kasashe 8 daga cikinsu su aiwatar da shi. Wannan tsarin yana daga cikin tsare tsaren kungiyar na dogon zango.

A halin yanzu dai farshin man yana kan $60 a cikin watan Afrilun da ya gabata, Sannan shi ne farashi mafi karanci tun shekaru 4 da suka gabata, kuma sana diyyar kara kudaden fiton da Trump yayi farashin ya tashi zuwa $65 kan ko wace ganga.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Al’ummar Fegin Mahe Sun Yi Zanga-zanga Kan Kisan Jama’a Da ‘Yan Bindiga Ke Yi

Daruruwan mazauna kauyen Fegin Mahe da ke yankin Ruwan Bore a karamar hukumar Gusau ta Jihar Zamfara, sun gudanar da zanga-zanga a gaban Gidan Gwamnati da ke Gusau, inda suka bukaci gwamnatin jihar ta dauki matakin gaggawa kan kisan gilla da ‘yan bindiga ke yi a yankinsu.

Masu zanga-zangar sun rike takardu masu dauke da rubuce-rubuce kamar su: “Muna bukatar zaman lafiya a yankunanmu” da “Gwamnati ta cika alkawarin da ta dauka”.

A cewar mazauna kauyen, harin ya faru ne da safiyar ranar Laraba, lokacin da wasu ‘yan bindiga dauke da manyan makamai suka afka wa kauyen, inda suka rika harbin mai-kan-uwa-da-wabi.

Al’ummar yankin sun bayyana harin a matsayin daya daga cikin mafi muni da suka taba fuskanta a ‘yan shekarun nan, wanda ya bar su cikin tsoro da fargaba.

Masu zanga-zangar sun ce manufarsu ita ce jawo hankalin gwamnati kan tabarbarewar tsaro a yankin da kuma bukatar daukar matakin gaggawa don dakile kisan fararen hula da ake ta yi ba kakkautawa.

Sun kuma koka da cewa har yanzu akwai gawarwakin wasu daga cikin mutanen da aka kashe a dajin, amma babu wanda ke iya dauko su saboda tsoron sake fuskantar hari  daga hannun ‘yan bindigar.

Har zuwa lokacin da ake hada wannan rahoto, ba a samu wata sanarwa ko martani daga gwamnatin jihar ba dangane da harin ko kuma zanga-zangar da aka gudanar.

 

Daga Aminu Dalhatu

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Al’ummar Fegin Mahe Sun Yi Zanga-zanga Kan Kisan Jama’a Da ‘Yan Bindiga Ke Yi
  • Aikin Zirga-Zirgar Jiragen Sama Ta Fasinja Ta Sin Ya Bunkasa Zuwa Sabon Matsayi
  • Babban Hafsan Sojin Iran Ya Ce: Iran Zata Sanya Duk Wanda Ya Dauki Matakin Wuce Gona Kanta Nadama
  • Eritrea ta gargadi Habasha game da yunkurin kafa tashar jiragen ruwa a cikin yankinta
  •  Kungiyar Malaman Musulmi Ta Yi Fatawar Wajabcin Kawo Karshen Killace Gaza
  • PSC Ta Amince Da Ɗaga Darajar Jami’an ‘Yan Sanda 12 Daga Matakin CP Zuwa AIG, Da Sauransu
  • Manoma A Kaduna Sun Yabawa Irin Masara Na TELA Saboda Juriyarshi Ga Kwari
  • Tsoffin Jami’an ‘Yan Sanda Sun Bukaci A fitar Da Su Daga Cikin Shirin Fansho
  • Gwamna Radda Da Makarrabansa Na Samun Kulawa A Asibiti Bayan Hatsarin Mota A Hanyar Daura
  • Kungiyar Hamas Ta Yi Suka Kan Kame ‘Yan Gwagwarmaya Da Hukumar Falasdinawa Ke Yi